| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Nijeriya ta gargaɗi 'yan ƙasarta da ke shirin zuwa Birtaniya kan tarzomar da ke faruwa
An kashe wasu mata matasa uku inda wasu yara biyar suka samu mummunan rauni a yayin wani harin wuƙa a lokacin da suka halarci wurin koyon rawa.
Nijeriya ta gargaɗi 'yan ƙasarta da ke shirin zuwa Birtaniya kan tarzomar da ke faruwa
'Yan sanda na ƙoƙarin hana masu zanga-zangar ɓallewa. / Hoto: Maitama Tuggar
5 Agusta 2024

Nijeriya ta gargaɗi 'yan ƙasarta da ke shirin tafiya Birtaniya bayan wata tarzoma ta adawa da bayar da mafaka ta ɓarke a Birtaniyar.

An kashe wasu mata matasa uku inda wasu yara biyar suka samu mummunan rauni a yayin wani harin wuƙa a lokacin da suka halarci wurin koyon rawa na Taylor Swift a ranar Litinin 29 ga watan Yuli.

Tarzoma ta ɓarke a garuruwa da birane da ke faɗin ƙasar, inda masu zanga-zanga dangane da adawa da baƙi masu shiga ƙasar suka yi fito-na-fito da 'yan sanda da masu zanga-zangar goyon bayan Musulmi a wasu lokutan.

"Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta fitar da sanarwa dangane da 'yan Nijeriya da ke shirin kai ziyara Birtaniya......ku guji duk wani gangamin siyasa, gangami da wuraren wasanni. A guji wuraren cunkoson jama'a da manyan taruka," in ji Ma'aikatar Harkokin Wajen Nijeriya a shafinta na X.

Firaministan Birtaniya Keir Starmer na shirin gudanar da taron gaggawa a ranar Litinin bayan wasu masu tsattsauran ra'ayi sun soma zanga-zanga a faɗin Birtaniya a ƙarshen makon da ya gabata inda aka kama ɗaruruwan mutane.

"Rikicin ya dauki wani sabon salo mummuna, kamar yadda rahotanni suka nuna a hare-haren da ake kai wa jami'an tsaro da kuma lalata ababen more rayuwa," in ji gargadin kan tafiye-tafiye da Nijeriya ta yi.

'Yan sandan Birtaniya sun dora alhakin tashin hankalin a kan magoya bayan kungiyoyin da ke da alaka da kungiyar English Defence League, mai adawa da Musulunci da aka kafa shekaru 15 da suka gabata, wadda ake alaƙanta magoya bayanta da tayar da rikici a wuraren kallon kwallon kafa.

Kai hare-hare kan masu neman mafaka

Mummunan tashin hankali ya ɓarke a ranar Lahadi a Rotterham, a arewacin Ingila, inda wasu masu zanga-zanga da suka rufe fuska suka farfasa tagogi a wani otel wanda aka rinƙa amfani da shi a matsayin matsuguni ga masu neman mafaka.

An raunata aƙalla 'yan sanda 10, daga ciki har da wani wanda aka sumar, in ji 'yan sandan South Yorkshire.

Haka kuma an yi rikici sosai a Bolton, da ke arewa maso yammacin Ingila, da Middlesbrough da arewa maso gabashin Ingila, wanda wuri ne da masu zanga-zanga suka fasa gidaje da motoci da kuma kama mutum 43.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata