| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Ambaliyar ruwa ta shafi fiye da mutum 700,000 a ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka: OCHA
Ambaliyar ruwa ta rusa ko kuma lalata gidaje sama da 60,000, inda ta tilasta wa mutane fiye da 54,000 ciki har da mata da yara barin muhallansu, in ji OCHA a wata sanarwa da ta fitar.
Ambaliyar ruwa ta shafi fiye da mutum 700,000 a ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka: OCHA
Chadi ce ƙasar da ambaliyar ruwan ta fi yi wa illa, inda ta shafi sama da mutum 245,000 cikin makonni kaɗan./Hoto: REUTERS
14 Agusta 2024

Ambaliyar ruwa da ta auku sakamakon sauyin yanayi ta shafi sama da mutum 700,000 a ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka a wannan shekarar kawo wannan lokaci, a cewar Ofishin Bayar da Jinƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya (OCHA) a ranar Talata.

Ambaliyar ruwa ta rusa ko kuma lalata gidaje sama da 60,000, inda ta tilasta wa mutane fiye da 54,000 ciki har da mata da yara barin muhallansu, in ji OCHA a wata sanarwa da ta fitar.

Kazalika ambaliyar ruwan ta rusa makarantu da asibitoci, lamarin da ya shafi samar da ilimi da kiwon lafiya.

Sanarwar ta ce mutum 72 ne aka bayar da rahoton mutuwarsu sakamakon nutsewa a ruwa sannan kusan mutum 700 sun jikkata.

Ƙasashen da ambaliyar ruwan ta shafa sun haɗa da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka, Chadi, Ivory Coast, Jamhuriyar Dimokuraɗiyya Kongo, Laberiya, Nijar, Nijeriya, Mali da Togo.

Chadi ce ƙasar da ambaliyar ruwan ta fi yi wa illa, inda ta shafi sama da mutum 245,000 cikin makonni kaɗan.

“A duk shekara, muna yin gargaɗi game da illolin sauyin yanayi da kuma tasirinsu kan rayuwar jama'a -- gidajensu, harkokin noma, yadda za su tura yaransu makaranta da samun kiwon lafiya,” in ji Charles Bernimolin, babban jami'in ONCHA a Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Ya ƙara da cewa, “Ya kamata a ɗauki matakai masu maa'ana domin tabbatar da ganin al'ummomi sun shirya wajen tunkarar wannan lamari ko kuma ma a yi rigakafin aukuwar bala'in".

Hukumomin da ke hasashen yanayi sun ce damunar 2024 za ta saukar da ruwan sama fiye da ƙima daga watan Yuni zuwa Satumba musamman a yankuna da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwa a ƙasashen yankin Sahel da na Yammacin Afirka.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta