| hausa
DUNIYA
3 MINTI KARATU
Harin da Isra'ila ta kai a makarantar MDD a Gaza ya kashe aƙalla mutum 14
Yaƙin Isra'ila a Gaza ya shiga rana ta 341, inda ta kashe kusan Falasɗinawa 41,084 – yanwacinsu mata da yara – tare da jikkata kusan 95,029 kuma wani ƙiyasi ya nuna cewa fiye da mutum 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa.
Harin da Isra'ila ta kai a makarantar MDD a Gaza ya kashe aƙalla mutum 14
Jami’an asibitin sun ce akalla mace daya da yara biyu na daga cikin wadanda suka mutu. Hoto: AFP
11 Satumba 2024

1522 GMT — Wani hari ta sama da Isra'ila ta kai ya kashe akalla mutane 14, ciki har da yara biyu, a makarantar Majalisar Dinkin Duniya da ta zama matsugunin iyalan Falasdinawa da ke tsakiyar Gaza, in ji jami'an asibiti.

Jami'ai daga asibitin al-Awda da ke Nuseirat sun ce sun karbi gawarwakin mutane 10 da harin ya kashe, sannan an kai wasu mutum hudu da suka mutu asibitin shahidan al-Aqsa da ke Deir al Balah.

Jami’an asibitin sun ce akalla mace daya da yara biyu na daga cikin wadanda suka mutu, sannan akalla mutane 18 sun samu raunuka.

More updates👇

1348 GMT — Adadin wadanda suka mutu a Gaza sakamakon harin da Isra'ila ta kai ya karu zuwa 41,084

Harin da sojojin Isra'ila suka kai a Gaza ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa akalla 41,084 tare da raunata 95,029 tun daga ranar 7 ga watan Oktoba, in ji ma'aikatar lafiya ta Falasdinu.

Akalla mutane 64 ne suka mutu a cikin sa'o'i 24 da suka gabata.

1256 GMT — Shugaban Iran ya caccaki Ƙasashen Yammacin duniya kan yakin Gaza da kuma goyon bayan Isra'ila

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya caccaki Kasashen Yammacin Duniya yana mai cewa Isra'ila na yin kisan kiyashi a yakin Gaza da kuma amfani da makaman Turai da Amurka wajen yin hakan.

Pezeshkian, wanda ya yi magana a Bagadaza a farkon ziyararsa ta farko a ketare tun bayan hawansa mulki, yana fatan karfafa alakar Tehran da Bagadaza a yayin da ake fama da rikici a yankin.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Hukumar Falasɗinawa ta yi maraba da shirin Kwamitin Tsaro na MDD kan Gaza
Kotun Bangladesh ta yanke wa Sheikh Hasina hukuncin kisa
Koriya ta Kudu ta nemi yin tattaunawar soji da Koriya ta Arewa don kaucewa rikicin kan iyaka
Trump ya sayi takardun lamuni na aƙalla dala miliyan 82 tun daga Agustan 2025 – Bayanai
Trump ya bayar da umarnin haramta wa masu ƙiba shiga Amurka
Fadan 'yan daba da gwamnati ya jawo asarar rayuka 1,200 a cikin wata uku a Haiti - MDD
Numfashi na mana wahala saboda gurbacewar iska a birnin New Delhi na India
An soke tashin jiragen sama fiye da 2,000 a Amurka yayin da harkokin gwamnati ke ci gaba da dagulewa
Zinarin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ke shigarwa ƙasarta daga Sudan ya ƙaru yayin da ake yaƙi
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila