| hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Afirka ta Kudu na neman 'girmama juna' a dangantakarta da Amurka
Afirka ta Kudu ta jaddada 'muhimmancin kyakkyawar alaka' da ke tsakaninta da Amurka.
Afirka ta Kudu na neman 'girmama juna' a dangantakarta da Amurka
Shugaban Kasar Amurka Joe Biden ya karbi bakuncin Shugaban KAsar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa a Fadar WHite House a watan Satumban 2022. Hoto: Reuters
20 Satumba 2024

Afirka ta Kudu na neman "ci gaba da kulla alaka bayyananniya" da Amurka kan batutuwan yankuna "bisa doron girmama juna", in ji Ministan Harkokin Waje Ronald Lamola.

Lamola ya bayyana haka a ranar Alhamis bayan kammala ziyarar da ya kai Amurka.

Ya isa Washington a makon da ya gabata a yayin da ake yada jita-jitar cewa jami'an diflomasiyyar Isra'ila na rokon 'yan majalisar dokokin Amurka su tirsasa wa Afirka ta Kudu ta janye karar kisan kiyashi da ta kai Tel Aviv a Kotun Kasa da Kasa (ICJ).

Afirka ta Kudu ta kai Isra'ila kara Kotun kasa da Kasa saboda hare-haren kan mai uwa da wabi da take kaiwa Gaza da aka mamaye wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 41,200 tun watan Oktoban bara.

Lamola ya gana da manyan masu ruwa da tsaki a Washington, ciki har da kwamitin Majalisar Wakilai Kan Afirka, Kwamitin Bakaken Fata, Kungiyar 'Yan Kasuwar Amurka da kungiyoyi masu zaman kansu.

'Yarda da sabanin ra'ayi'

Ministan harkokin wajen ya jaddada muhimmancin cigaban sauyin da ake samu a alakar da ke tsakanin Afirka ta Kudu da Amurka, inda ya kuma zayyano fannonin da ake hada kai.

"Ana matsa wa gaba, za kuma a bi hanyoyin dorewar tasarin dangantakar siyasa a koyaushe," in ji Lamola.

Da yake jawabi ga Babban Taron Shekara-Shekara Karo na 53 na 'Yan Majalisar Dokoki Bakaken Fata a Washington a makon da ya gabata, Lamola ya bayyana cewa "Mu yi mu'amala duk da bambance-bambance amma kuma dole mu yarda ana iya saba wa juna."

Ya ce "Ba za mu fada wa Amurka abinda za ta yi ko me muke tsammani ta fada mana mu yi ba."

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata