| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Alaƙar Turkiyya da Sudan na ci gaba da bunƙasa a kowace rana: Erdogan
Shugaban kasar Turkiyya Erdogan wanda ke birnin New York domin halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79, yana ci gaba da gudanar da harkokinsa a Gidan Turkiyya da ke birnin.
Alaƙar Turkiyya da Sudan na ci gaba da bunƙasa a kowace rana: Erdogan
A ganawar da suka yi a ranar Laraba, sun tattauna kan dangantakar kasashensu, da kuma batutuwan shiyyoyi da na duniya baki daya.
26 Satumba 2024

"Alakar Turkiyya da Sudan na ci gaba da bunkasa a kowace rana kuma hadin kai tsakanin kasashen biyu zai kara karfi," in ji Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a yayin ganawarsa da shugaban majalisar mulkin kasar Sudan Abdel Fattah al Burhan a Gidan Turkiyya da ke birnin New York na Amurka.

A ganawar da suka yi a ranar Laraba, sun tattauna kan dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma batutuwan da suka shafi shiyyoyi da na duniya baki daya.

Har ila yau, a ranar Talata, yayin jawabinsa a babban taron MDD na shekara-shekara, Erdogan ya ce "Dole ne a kawo karshen rikicin da ake fama da shi a Sudan da wuri-wuri, kuma mu ƙara zage damtse wajen cim ma wannan buri."

Mummunan yanayi a Sudan

Kasar Sudan dai ta sha fama da fada tsakanin sojojin Sudan da kuma dakarun Rapid Support Forces (RSF).

Akalla mutum 12,260 ne aka kashe yayin da fiye da 33,000 suka jikkata a rikicin da ya fara a watan Afrilun 2023, a cewar alkaluman MDD.

Ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya OCHA ya ce a yayin da al'amura ke ci gaba da tabarbarewa a fadin kasar Sudan, ana tilasta wa mata da kananan yara da daukacin iyalai ƙaurace wa gidajensu, tare da barin komai.

OCHA ta ruwaito cewa a halin yanzu Sudan na fuskantar "mafi girman karancin abinci a cikin shekaru 20."

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta duniya (IOM) ta ce tun bayan da aka fara yakin Sudan a watan Afrilun 2023, sama da mutum miliyan 7.7 ne suka rasa matsugunansu.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata