| hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Turkiyya ta yi 'jimamin' haɗarin jirgin ruwa a Nijeriya
Ma'aikatar harkokin waje ta Turkiyya ta miƙa ta'aziyyarta ga al'umma “'yan uwa kuma abokai” da ke Nijeriya.
Turkiyya ta yi 'jimamin' haɗarin jirgin ruwa a Nijeriya
Nigerian authorities launched a search a rescue operation after the boat accident on Tuesday. Photo: NEMA/X
5 Oktoba 2024

Turkiyya ta miƙa ta'aziyyarta kan waɗanda suka rasu sakamakon mummunan haɗarin jirgin ruwa a Nijeriya.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da rashin rayuka da aka samu bayan nutsewar jirgin ruwa da ke ɗauke da fasinjoji kimanin 300 a Nijeriya,” in ji M'aikatar Harkokin Waje ta Turkiyya a wata sanarwa ranar Juma'a.

Ma'aikatar ta miƙa ta'aziyyarta ga al'umma “'yan uwa kuma abokai” da ke Nijeriya.

Jirgin ruwan yana ɗauke da mutane 300 da ke dawowa daga taron addini yayin da jirgin ya kife, a jihar Neja da ke arewa ta tsakiya a daren Talata.

Gano gawarwaki

Aƙalla gawarwaki 60 aka gano yayin da aka ceto mutane 160 bayan afkuwar haɗarin, cewar wani jami'i ranar Laraba.

Haɗarin na Kogin River Niger ya faru a wuraren Al'ummar Gbajibo, in ji Jibril Abdullahi Muregi, shugaban ƙaramar hukumar Mokwa. An kwaso gawarwaki da dama ranar Juma'a yayin da ake ci gaba da aikin ceto.

Fasinjojin, yawancinsu mata da yara, suna kan hanyarsu ta zuwa bikin Maulidi.

Hukumomi sun ce an samo ƙarin gawarwaki ranar Juma'a, kuma ana ci gaba da aikin ceto, kwanaki bayan afkuwar haɗarin.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan