AFIRKA
2 MINTI KARATU
Kwalara ta kashe mutum 359 a watanni tara a Nijeriya
NCDC ta ce mutane 359 ne suka mutu daga watan Janairu zuwa Satumban bana, inda a irin wannan lokaci na shekarar da ta gabata aka samu rasa rayuka 106.
Kwalara ta kashe mutum 359 a watanni tara a Nijeriya
Cutar kwalara na sanadin mutuwar dubban yara a fadin duniya. Hoto/Reuters
7 Oktoba 2024

Fiye da mutum 350 ne suka mutu sakamakon kwalara a watanni tara na shekarar nan, ƙari da kashi 239 idan aka kwatanta da alƙaluman shekarar da ta gabata a daidai wannan lokaci, in ji Cibiyar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Nijeriya (NCDC).

Cutar kwalara da ake ɗauka daga ruwan sha mara tsafta, ta zama ruwan dare a Nijeriya inda hukumomin lafiya ke cewa babu tsaftataccen ruwan a yankunan karkara da unguwannin marasa galihu da ke birane.

NCDC ta ce mutane 359 ne suka mutu daga watan Janairu zuwa Satumban bana, inda a irin wannan lokaci na shekarar da ta gabata aka samu rasa rayuka 106.

Adadin waɗanda suka kamu da cutar ta kwalara ya ƙaru zuwa 10,837, daga 3,387 a bara, inda mafi yawan waɗanda suka kamu yara ne 'yan ƙasa da shekaru biyar.

Lagos, babban birnin kasuwanci na Nijeriya ne ke da adadi mafi yawa na mutanen da suka kamu da cutar, in ji NCDC.

Mahukunta a Borno da ke arewa maso-gabashin Nijeriya a ranar Juma'a sun bayyana ɓarkewar cutar a jihar, wadda ta yi fama da ambaliyar ruwan da ta raba mutane miliyan biyu da matsugunansu.

MAJIYA:Reuters
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar