| Hausa
TURKIYYA
3 MINTI KARATU
Erdogan ya yi gargaɗi kan ƙarfin ikon 'yan koren Isra'ila a manyan jami'o'in duniya
"Babu tantama cewa 'yan koren Isra'ila ne ke riƙe da iko da manyan jami'o'in duniya da sunan bayar da tallafin kuɗi," in ji shugaban Turkiyya.
Erdogan ya yi gargaɗi kan ƙarfin ikon 'yan koren Isra'ila a manyan jami'o'in duniya
A kisan kiyashin Gaza, gwamnatocin Yammacin duniya ba su tabuka abin a zo a gani ba, sun zubar da girmansu wajen kare Isra'ila," in ji shugaba Erdogan. / Hoto: AA / Others
9 Oktoba 2024

Ta'annatin da Isra'ila ke aikatawa a yankin Gaza na Falasɗinu ya bayar da gudunmawa wajen fitowa fili a fahimci yadda 'yan koren Isra'ila ke da iko kan manyan jami'o'in duniya, in ji shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan.

"Mun shaida irin wannan abin kunyar inda 'yan sanda suka dinga musguna wa ɗaliban da suka ce 'ana aikata kisan kiyashi a Gaza', shugaba Erdogan ya bayyana haka a ranar Talata a yayin taron ɗabuwar shekarar karatu ta 2024/2025 a Ankara.

Ya kuma ja hankali kan yadda aka tursasa wa shugabannin jami'o'i da suka bayar da damar yin zanga-zangar adawa da kisan Falasɗinawa yin murabus, aka azabtar da su tare da titsiye su a gaban majalisar dokokin a Amurka.

Ya jaddada cewa "Babu wani suka ko bayyana ra'ayi game da Falasɗinawa aka yarda da shi. Ya zama babu tantamar cewa 'yan koren Isra'ila ne ke riƙe da iko da manyan jami'o'in duniya inda suke fakewa da bayar da tallafin kuɗaɗe."

Shugaban na Turkiyya ya kuma soki gwamnatocin ƙasashen Yammacin duniya bisa gazawa wajen kawo ƙarshen kisan kiyashi a Gaza tsawon shekara guda, yana mai cewa sun zubar da ƙimarsu "a ƙoƙarin da suke yi na kare Isra'ila".

Yaƙi da dukkan 'yan'adam

Da take ci gaba da saɓa wa matakin da Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ɗauka na kiran da a tsagaita wuta a Gaza, Isra'ila na ci gaba kai munanan hare-hare Gaza, tana mai fakewa da harin da ƙungiyar tirjiya ta Falasɗinawa Hamas ta kai mata a ranar 7 ga Oktoban 2023.

Hare-Haren na Isra'ila sun tsugunar da kusan dukkan jama'ar yankin da ci gaba d fuskantar mamayar da ta janyo karancin abinci, tsaftataccen ruwan sha, da magunguna.

Ƙoƙarin shiga tsakani da Amurka, Masar da Qatar ke jagoranta don a tsagaita wuta a Gaza da yin musayar fursunoni tsakanin Hamas da Isra'ila ya ci tura saboda yadda Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dakatar da yaƙin.

Yaki na tsawon shekara guda da Tel Aviv ke yi a Gaza ya yi ajalin mutane 42,000. Isra'ila na fuskantar tuhumar aikata kisan kiyashi a Kotun Kasa da Kasa saboda ta'annatin da ta aikata a yankin, da ke da Falasdinawa sama da miliyan biyu.

A gefe guda, hare-haren Isra'ila a Lebanon tun daga 2023 zuwa yau sun yi sanadiyar mutuwar sama da mutum 2,000 inda aka raba wasu milayan 1.2 da matsugunansu.

Rumbun Labarai
Adadin jama'ar Turkiyya ya kai miliyan 86 a 2025 yayin da jama'ar ƙasar ke ƙara yawa
Matar Shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun ƙara jaddada ƙawance a Istanbul
Turkiyya ta kama jami'an Mossad na Isra'ila biyu a Istanbul kan leƙen asiri
Shugaba Erdogan ya tuna da girgizar ƙasa, ya ce ‘Turkiyya ta cika alkawarinta‘ na sake gina gidaje
Turkiyya ta bunƙasa taimakon da ta ke ba Somaliya na sojojin sama da ƙasa don yaƙi da ta'addanci
Shugaban Turkiyya Erdogan ya gana da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a Riyadh
Shugaban Turkiyya zai ziyarci Saudiyya da Masar a cikin wannan makon
Fidan na Turkiyya ya gargaɗi Amurka kan kai wa Iran hari, ya ce Tehran a shirye take ta tattauna
Zaman lafiyar Iran na da muhimmanci ga tsaron yankin: Turkiyya
Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta'addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu
Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hidan ya yaba da "Kwamitin Zaman Lafiya" na Gaza
Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan
Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sa hannu na 'Hukumar Zaman Lafiya' ta Gaza a Switzerland
An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya
‘Syria ta ‘yan Syria ce’: Erdogan ya yaba da yarjejeniyar zaman lafiya ta Damascus