AFIRKA
2 MINTI KARATU
Chadi ta yi barazanar ficewa daga ƙawancen dakarun yankin tafkin Chadi
Kimanin sojojin Chadi 40 ne aka kashe a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai yankin a karshen watan Oktoba.
Chadi ta yi barazanar ficewa daga ƙawancen dakarun yankin tafkin Chadi
Deby

Shugaban Chadi, Mahamat Idriss Deby, ya yi barazanar cewa ƙasarsa za ta fice daga dakarun kawancen MNJTF na yankin wanda Deby ya ce ƙawancen ya kasa kawo karshen yan bindiga a yankin tafkin Chadi.

Deby ya yi bayanin ne a ranar Lahadi a lokacin da ya kai ziyara yankin da ya hada da wani bangare na yammacin Chadi da kuma Nijeriya da Nijar da kuma Kamaru.

Kimanin sojojin Chadi 40 ne aka kashe a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai yankin a karshen watan Oktoba.

Yayin da yake shelar kaddamar da hari kan maharan, Deby ya ce yana tunanin janyewa daga hadakar dakaru ta MNJTF, wadda ta hada da sojoji daga kasashe masu makwabtaka da tafkin Chadi.

Aikin dakarun hadakan ya kasance mai sarkakiya saboda rarrabuwan kawuna da kuma rashin hadin kai, amma ficewar Chadi za ta kasance babban koma-baya saboda sojojinta na cikin wadanda aka fi girmamawa a yankin, in ji kamfanin dillacin labaran Reuters.

Deby ya bayyana cewa "rashin hadin kai wajen tunkarar abokin gaba, lamarin da ake gani a fagen daga. Dakarunnan da aka samar domin hada karfi da karfe da kuma musayan bayanan sirri, da alama sun yi rauni."

Masu tada kayar baya ciki har da ISWAP da Boko Haram sun sha kai hare-hare yankin na Tafkin Chadi tun lokacin da rikicin Boko Haram da aka fara a arewa maso gabashin Nijeriya a shekarar 2009 ya kai yammacin Chadi.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar