| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Ba ma sayar da gurɓataccen man fetur—NNPC
Soneye ya ce ba zai yiwu a ce an sayi man daga gidan NNPC ba domin gidajen kamfanin ba sa sayar da mai a galon ko jarkoki.
Ba ma sayar da gurɓataccen man fetur—NNPC
Nijeriya ta dade tana shigowa da man fetur tun lokacin da matatun mai mallakar ƙasar suka daina aiki . / Hoto: NNPCL X
8 Nuwamba 2024

Kamfanin man Nijeriya, NNPC, ya ce ba ya sayarwa ko hulɗa da gurɓataccen man fetur.

Wata sanarwar da babban daraktan watsa labaran kamfanin, Oluemi Soneye, ya sanya wa hannu, ta ce “ɓangaren NNPC da ke kula da gidajen man kamfanin ba ya hulɗa da gurbataccen man fetur domin yana biyayya ga ƙa’idoji da matakan tabbatar da inganci a ko wane matakin aikinsa domin tabbatar da cewa yana samar da man fetur mai inganci a gidajen mansa.”

Sanarwar ta biyo bayan fitowar wani faifan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta inda wani direba ya ce ya sayi gurɓataccan mai a wani gidan man NNPC dake kusa da wata babbar gada a Keffi, jihar Nasarawa.

Soneye ya ce ba zai yiwu a ce an sayi man daga gidan man NNPC ba domin gidajen kamfanin ba sa sayar da mai a galan-galan ko jarkoki.

“Mun gudanar da bincike a dukkannin gidajen manmu kuma mun tabbatar da cewa wannan iƙirarin ba gaskiya ba ne” a cewar daraktan watsa labaran NNPC .

Soneye ya buƙaci jama’a su yi watsi da zargin da ke cikin bidiyon yana mai ƙarawa da cewa masu yaɗa zargin da ba shi da tushe, ba sa kishin ƙasarsu.

Maganar gurɓataccen man fetur dai ya ja hankalin ƴan Nijeriya a lokacin da sabuwar matatar mai da attajirin Afirka, Aliko Dangote, ya gina ya yi iƙirarin cewa wasu na shigowa da man fetur mara inganci cikin ƙasar maimakon su sayi man fetur mai kyau daga matatar.

Nijeriya ta dade tana shigowa da man fetur tun lokacin da matatun mai mallakar ƙasar suka daina aiki duk da cewa ƙasar tana cikin ƙasashen da suka fi samar da ɗanyen mai a kasuwannin duniya.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta