Mutum 13 sun mutu sakamakon ruftawar wajen haƙar ma'adanai a Nijeriya
Wani jami’in gwamnati a jihar, Joshua Riti, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Anadolu na Turkiyya a ranar Talata cewa wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru tsakanin 18 zuwa 30 ne kuma ‘yan karamar hukumar Bassa ne.
Akalla mutane 13 ne suka mutu sakamakon ruftawar wani wurin hakar ma'adinai a jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya.
Wani jami’in gwamnati a jihar, Joshua Riti, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Anadolu na Turkiyya a ranar Talata cewa wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru tsakanin 18 zuwa 30 ne kuma ‘yan karamar hukumar Bassa ne.
Ya kara da cewa, rugujewar ta afku ne a ranar Asabar a kan iyakokin kananan hukumomin Bassa, Jos ta Kudu, da Jos ta Arewa, inda wadannan matasa suke neman abin dogaro da kai a cikin ramin hakar ma’adinai.
A baya-bayan nan masu hakar ma’adinai 22 ne suka mutu sakamakon ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a wani haramtaccen wuri da ke cikin wani wurin gandun namun daji da ke yankin karamar hukumar Gashaka a jihar Taraba da kuma karamar hukumar Toungo a jihar Adamawa.