| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Kusan mutum 200 da kwale-kwale ya kife da su a Kogin Neja sun yi ɓatan-dabo — hukumomi
Hukumar Kula da Hanyoyin Sufurin Ruwa na Cikin Gida ta Nijeriya ta ce har yanzu ko mutum ɗaya ba a gano ba bayan wani kwale-kwale ya kife da kusan mutum 200 a ranar Juma'a.
Kusan mutum 200 da kwale-kwale ya kife da su a Kogin Neja sun yi ɓatan-dabo — hukumomi
Gomman mutane ke mutuwa a Nijeriya duk shekara sakamakon hatsarin kwale-kwale. Hoto/Reuters
1 Disamba 2024

Har yanzu masu aikin ceto sun gaza gano ko mutum guda a cikin kusan mutum 200 waɗanda suka yi ɓatan-dabo bayan wani kwale-kwale ya kife da su a Jihar Kogi da ke Nijeriya, kamar yadda wani jami’i a ƙasar ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu.

Suleiman Makama, wanda shi ne mai magana da yawun Hukumar Kula da Hanyoyin Sufurin Ruwa na Cikin Gida ta Nijeriya ya shaida cewa ma’aikatan da aka aika hanyar ruwa ta Dambo-Ebuchi da ke Kogin Neja wanda a nan ne kwale-kwale ya kife a ranar Juma’a sun gaza gano ko mutum ɗaya a raye ko akasin haka.

“Har yanzu ba mu gano wani daga cikin fasinjoji daga cikin kogin ba. Ana ci gaba da gudanar da aikin ceto,” kamar yadda Makama ya bayyana.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da gudanar da ayyuka nan da kwanaki masu zuwa. Kusan fasinjoji 200 galibi mata ‘yan kasuwa ne da manoma da kuma mazauna yankin da suka shiga kwale-kwale daga jihar ta Kogi da sanyin safiyar Juma’a, suka ɓace bayan da kwale-kwalen da suke ciki ya kife suna dab da isa wurin da za su sauka.

Ana yawan samun matsalar kifewar kwale-kwale a Nijeriya a duk shekara.

Ko a kwanakin baya sai da masu zuwa taron maulidi fiye da 100 suka rasu bayan kwale-kwalen da suke ciki ya kife da su a hanyar zuwa Jihar Neja.

Ana yawan alaƙanta kifewar kwale-kwale a Nijeriya da yin lodi fiye da ƙima da rashin bin ƙa’idojin da suka dace waɗanda suka shafi sufurin ruwa.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta