| hausa
KASUWANCI
2 MINTI KARATU
Gwamnatin Nijar ta ƙwace ikon gudanar da kamfanin  Orano na Faransa
Orano ne ya mallaki kashi 63.4 na lasisi a kamfanin Somair da ke haƙar ma'adinai a Nijar, yayin da gwamnatin Nijar take da kashi 36.6.
Gwamnatin Nijar ta ƙwace ikon gudanar da kamfanin  Orano na Faransa
Orano ne ya mallaki kashi 63.4 na lasisi a kamfanin Somair da ke haƙar ma'adinai a Nijar, yayin da gwamnatin Nijar take da kashi 36.6. / Photo: AFP
4 Disamba 2024

Kamfanin makamashin nukiliyar Faransa Orano ranar Laraba ya ce hukumomin sojin Jamhuriyar Nijar sun ƙwace ikon "gudanar" da tasharsa ta makamashin yuraniyom da ke ƙasar ta Yammacin Afirka.

Da ma dai a watan Oktoba ne kamfanin na Orano ya sanar da dakatar aiki a tasharsa da ke Nijar sakamakon abin da ta bayyana a matsayin ƙarin matsin lamba da yake fuskanta daga hukumomin ƙasar a fannin gudanarwa da harkokin kuɗi.

Orano ne ya mallaki kashi 63.4 na lasisi a kamfanin Somair da ke haƙar ma'adinai a Nijar, yayin da gwamnatin Nijar take da kashi 36.6.

"Kamfanin Orano ya kwashe watanni da dama yana gargaɗi game da katsalandan ɗin da yake fuskanta wajen tafiyar da harkoki a Somair," in ji wata sanarwa da kamfanin na Faransa ya fitar.

"Ba a aiwatar da matakan da kamfanin ya amince da su a wurin taron manyan shugabanninsa, don haka, a yau, Orano yana tabbatar da cewa hukumomin Nijar sun karɓe ikon gudanar da Somair," in ji sanarwar.

A watan Yuni, hukumomin Nijar sun soke yarjejeniyar da aka ƙulla da Orano domin haƙo yuraniyom a mahaƙar ma'adinai ta Imouraren, wacce ke da nauyin aƙalla tan 200,000.

Gwamnatin sojin Nijar, wadda ta hau kan mulki a watan Yulin da ya gabata, ta ce za ta sabunta dokokin haƙar ma'adinai na ƙasar.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Kamfanin simintin Dangote ya fara aiki a ƙasar Ivory Coast
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri