| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Mutum 70 sun yi ɓatan-dabo sakamakon kifewar jirgin ruwa a Morocco
Dubban 'yan ci-rani ne ke yunkurin tsallakawa cikin teku daga gabar tekun Afirka a kowace shekara da fatan shiga Turai, galibi a suna ƙoƙrin yin haka ne a cikin kwale-kwale ko jirgin ruwa maras nagarta.
Mutum 70 sun yi ɓatan-dabo sakamakon kifewar jirgin ruwa a Morocco
Fiye da 'yan ci rani 10,400 suka rasu a yayin da suke ƙoƙarin isa Faransa a 2024. / Hoto: Reuters
27 Disamba 2024

Nutsewar wani jirgin ruwa ɗauke da 'yan ci-rani a Tekun Morocco a ranar 19 ga watan Disamba ya yi sanadin ɓacewar mutum 70, ciki har da 25 daga kasar Mali, in ji gwamnatin kasar a ranar Alhamis.

Kusan 'yan ci-rani 80 ne a kan jirgin wanda ke hanyarsa ta zuwa Sifaniya, "akwai matasan Mali 25 waɗanda aka gano ya rutsa da su" kamar yadda gwamnatin ta bayyana a cikin wata sanarwa.

Dubban 'yan ci-rani ne ke yunkurin tsallakawa cikin teku daga gabar tekun Afirka a kowace shekara da fatan shiga Turai, galibi a suna ƙoƙrin yin haka ne a cikin kwale-kwale ko jirgin ruwa maras nagarta.

Tafiya mai hatsari

Fiye da baƙin haure 10,400 ne suka mutu a kokarin isa Sifaniya tun daga shekarar 2024, ciki har da wani adadi mai yawa da ke kan hanyar zuwa tsibirin Canary, in ji wata kungiya mai zaman kanta ta Sifaniya, Caminando Fronteras a cikin wani rahoto a ranar Alhamis.

Hakan na nufin a matsakaicin lissafi aƙalla mutum 30 a rana.

A tafiya ta kusa-kusa, tsibirin na Canary na da nisan kilomita 100 daga gaɓar Tekun Arewacin Afirka.

Hanya mafi ƙanƙanta ta fara ne daga garin Tarfaya da ke kudancin Maroko zuwa Fuerteventura da ke tsibirin Canary.

Hanyoyin ruwa na Tekun Atlantika suna da matuƙar haɗari inda jiragen ruwa da dama waɗanda ake cikawa maƙil, waɗanda kuma ba su da kayayyakin aiki.

Wasu daga cikin jiragen ruwan da ke barin bakin ruwa a Afirka na da nisan kusan kilomita 1,000 daga tsibirin na Canary.

Mali ta jima tana fama da matsalolin tsaro tun daga shekarar 2012, inda take fuskantar hare-hare daga masu iƙirarin jihadi waɗanda ke da alaƙa da al-Qaeda, da kuma ƙungiyoyin 'yan aware.

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi kiyasin cewa tun daga shekara ta 2014 zuwa yanzu fiye da bakin haure 16,400 ne suka mutu a kokarin shiga Turai daga Afirka, adadin da ya hada da wadanda ke kan hanyar zuwa tsibirin Canary.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan