AFIRKA
3 MINTI KARATU
Kayode Egbetokun: Me ya sa Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya ke ci gaba da zama kan kujerarsa bayan ya cika shekara 60?
Wasu na zargin cewa an tsawaita wa'adin  Kayode Egbetokun a kan kujerar Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya bayan ya cika shekara 60 domin a yi amfani da shi wajen cim ma muradu na siyasa a zaɓen shekarar 2027.
Kayode Egbetokun: Me ya sa Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya ke ci gaba da zama kan kujerarsa bayan ya cika shekara 60?
Babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun
31 Janairu 2025

Zancen cancantar Sufeto Janar na ‘yan sandan Nijeriya ya ci gaba da zama kan kujerarsa bayan ya cika shekara 60 na daɗa jan hankalin jama’a inda 'yan gwagwarmaya ke cewa ya kamata a ce ya yi murabus.

Ranar 31 ga watan Oktoban shekarar 2023 ne dai Kayode Egbetokun ya kama aiki a matsayin sufeto janar na ‘yan sandan Nijeriya.

Sai dai kuma bayan shekara da kama aikin a matsayin shugaban ‘yan sandan ƙasar ne Kayode ya cika shekara 60 da haihuwa, wato ranar 4 ga watan Satumba.

Wannan ne ya sa ‘yan gwagwarmaya irin su Omoyele Sowore, wanda ya yi takarar shugaban ƙasar Nijeriya a baya, ke ganin ya kamata a ce Kayode ya sauka daga kujerarsa ta shugaban ‘yan sandan ƙasar.

"Ba haka abin yake ba"

Sai dai kuma Antoni Janar kuma Ministan Shari'a na ƙasar, Lateef Fagbemi, da ma rundunar ‘yan sandan ƙasar sun ce lamarain ba haka yake ba.

A wata sanarwar da ya fitar, Fagbemi ya ce an riga an sauya dokar aikin ‘yan sandan Nijeriya ta yadda Sufeto Janar na ‘yan sanda zai kammala wa’adin mulkinsa na shekara huɗu kafin ya yi murabus ko da ma ya cika shekara 60.

“Wannan ya tsawaita wa’adin aikin Egbetokun zuwa ranar 31 ga watan Oktoban shekarar 2027 domin ya cika wa’adinsa na shekara huɗu da aka ba shi,” in ji sanarwar da ministan ya fitar.

“Saboda a kauce wa shakku, ci gaba da zaman Egbetokun a ofis ya dace da dokar aikin ‘yan sandan Nijeriya da aka gyra a shekarar 2024 wadda ta bai wa wanda ke kan kujerar damar ya yi aiki na shekara huɗu daga ranar da aka naɗa shi Sufeto Janar, a nan, daga ranar 31 ga watan Oktobar shekarar 2023,” a cewar Lateef.

Kazalika shi ma mai magana yawun rundunar ‘yan sandan Nijeriya, Olumuyiwa Adejobi ya ambato sashen na 7, sakin layi na 6 cikin dokar aikin ‘yan sandan Nijeriyar wanda ke cewa “wanda aka naɗa a matsayin Sufeto Janar na ‘yan sanda zai kwashe shekara huɗu yana aikin.”

A sanarwar da ya fitar a shafin Facebook na rundunar ‘yan sandan Adejobi ya ce iƙirarin cewa Egbetokun bai dace da ci gaba da kasancewa shugaban ‘yan sandan Nijeriya ba, ba shi da tushe balle makama, yana mai ƙarawa da cewa an yi zargin ne domin yi wa shugabancinsa zagon-ƙasa.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci