| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
Guardiola ya ce zai sallama Kofin Firimiya idan Man City ta sha kashi a hannun Arsenal
Masu sharhi kan gasar Firimiya na cewa wasan na ƙarshen mako tsakanin Manchester City da Arsenal zai fayyace makomar gasar ta kakar 2025-26.
Guardiola ya ce zai sallama Kofin Firimiya idan Man City ta sha kashi a hannun Arsenal
Pep Guardiola shi kaɗai ne manajan da ya taɓa lashe kofin Firimiya sau huɗu a jere. / Reuters

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce kofin Firimiya zai kuɓuce musu idan dai Arsenal ta doke su a wasansu na gaba da za a yi ranar Lahadi mai zuwa.

Gabanin wasan, Arsenal na saman teburi kuma ta ba City tazarar maki shida, duk da cewa City na da kwantan wasa guda, yayin da ya rage makonnin wasa shida a kammala kakar bana.

Da yake jawabi gabanin wasan, Guardiola ya ce, "Idan muka yi rashin nasara [a hannun Arsenal], komai ya ƙare kenan [mun bar musu kofin Firimiya]. Suna da ƙarfi sosai a duka ɓangarori.”

Idan City ta doke Arsenal, hakan na nufin sun cike giɓin maki uku sannan sun karɓi damar kamo Arsenal a hannunsu. Amma Guardiola ya ce kada a ce shikenan su za su ci kofin kai-tsaye.

Ya yi nuni da cewa akwai sauran aiki a gaba kuma ba mai sauƙi ba, kasancewar akwai yiwuwar ɓarar da maki a gaba, musamman ganin irin ƙungiyoyin da za su kara da su.

Ya ce, "Wasanninmu da ke tafe na da haɗari, akwai wasan Everton a gidansu, Bournemouth a gidansu, sannan Aston Villa a ƙarshe a gidanmu. Ga Burnley da Crystal Palace da Brentford a gidanmu.

Masu sharhi kan gasar ta Firimiya na cewa wasan na ƙarshen mako tsakanin Manchester City da Arsenal zai fayyace makomar gasar ta kakar 2025-26.

Baya ga wasan na gaba, hankalin City na kan wasan samifainal na kofin FA da za su kara da Southampton, yayin da Arsenal ke fafutukar lashe kofin Firimiya da kuma na Zakarun Turai inda za su kara da Atletico Madrid a samifainal.

Rumbun Labarai
Neymar ya yi dambe da ɗan Robinho a haduwarsu ta farko a filin atisaye na Santos
CAF ta tabbatar da ranakun gasar AFCON 2027 a Kenya, Tanzania da Uganda
Iran za ta buga wasannin Gasar Kwallon Kafa ta Duniya a Amurka duk da rikici, in ji FIFA
Tsohon ɗanwasan Nijeriya Eneramo ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin wasan sada zumunta
Iran 'ba ta ƙarƙare yanke hukunci' kan halartar Kofin Duniya na 2026 a Amurka ba
Tottenham na neman masanin lafiyar tunani ga ‘yanwasanta, don gujewa fadowa daga gasar Firimiya
'Na yi imanin Arsenal ce za ta ɗaga Kofin Firimiya' - Arsene Wenger
Nijeriya ta yi maraba da 'yarwasan tsere, Favour Ofili wadda aka hana ta sauya kasar da take wakilta
Shugaban FIFA ya ce akwai ‘tabbacin’ Iran za ta halarci Gasar Cin Kofin Duniya
Hukumar FA ta ci tarar Harry Maguire saboda rashin ɗa'a a wasan Man United da Bournemouth
UEFA ta yi watsi da korafin Barcelona kan wasan da Atletico Madrid ta doke su
Masoyin Arsenal ɗan Uganda na barazanar kai Gunners kotu kan damuwar da ya shiga bayan shan kaye
Danwasan Ghana, Kudus ya samu rauni a Tottenham, zai iya gaza zuwa gasar Kofin Duniya ta 2026
Anthony Joshua 'zai koma damben boksin' bayan mummunan hatsarin mota
Mbappe da Vinicius za su koma aiki tare a wasan Real Madrid da Bayern Munich
Ghana ta kori kocinta Addo makonni gabanin gasar cin kofin duniya
Ina Mo Salah zai koma daga Liverpool?
Nijeriya ta doke Iran a wasan sada zumunta da suka buga a Turkiyya
Lukaku ya ƙi komawa atisaye a Napoli bayan janyewa daga buga wa ƙasarsa Belgium wasa
Batun kofin AFCON: Me zai faru da ƙwallon ƙafa a Afirka bayan tataɓurza kan Senegal?