| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yan Nijeriya 'yan ci-rani 65,500 da suka makale a ƙasashen waje aka ceto cikin shekaru tara
Da yake jawabi a wani taron horar da ‘yanjarida kan rahoton hijira a Legas, hukumar ta bayyana cewa an kuma inganta yanayin tunani da zamantakewa da tattalin arziki na fiye da mutum 30,000 da suka dawo ƙasar domin sake gina rayuwarsu.
'Yan Nijeriya 'yan ci-rani 65,500 da suka makale a ƙasashen waje aka ceto cikin shekaru tara
'Yan Nijeriya 'yan ci-rani 65,500 da suka makale a ƙasashen waje aka ceto cikin shekaru tara / NEMA

Kungiyar Ƙasa da Ƙasa mai kula da Kaura, IOM ta ce ta ceto fiye da ‘yan Nijeriya 65,500 da suka makale a ƙasashen waje cikin shekaru tara da suka gabata, lamarin da ke nuna girman ƙalubalen ƙaurar da ba ta dace ba da ƙasar ke fuskanta.

Da yake jawabi a wani taron horar da ‘yanjarida kan rahoton hijira a Legas, hukumar ta bayyana cewa an kuma inganta yanayin tunani da zamantakewa da tattalin arziki na fiye da mutum 30,000 da suka dawo ƙasar domin sake gina rayuwarsu.

IOM ta ce tana ƙara ƙoƙari wajen inganta hanyoyin hijira masu aminci da na doka, tare da yin kira ga ƙarin wayar da kai ga jama’a da kuma ingantaccen rahoton kafafen yaɗa labarai kan batutuwan hijira.

“Za mu kawo ƙarin bayani kan adadin, labaran mutane da kuma abin da ake yi domin dakile hanyoyin hijira masu haɗari,” in ji ta a wata sanarwa da ta biyo baya.

Wannan ci gaban ya biyo bayan ƙara tsaurara matakan yaƙi da baƙin haure a ƙasashe da dama a duniya.

Kwanan nan, Amurka ta ƙara tsaurara matakan korar ‘yan ƙasashen waje, ciki har da ‘yan Nijeriya, inda bayanan Ma’aikatar Tsaron Gida ta Amurka (DHS) suka nuna cewa an gano ɗaruruwan ‘yan Nijeriya da ke fuskantar umarnin kora ko kuma da laifukan da suka kai ga korarsu.

Wannan mataki na daga cikin ƙarin tsauraran dokoki da gwamnatin Amurka ke aiwatarwa kan baƙin haure da kuma masu laifuffuka masu tsanani.