| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Shirin zai taimaka wajen gano da horar da matasa manyan gobe ‘yan Nijeriya tare da samar da hanyar tallafawa ƙirƙire-ƙirƙirensu masu mahimmaci a fannonin Kimiyya da Fasaha da Injiniyanci da Lissafi da kuma Kimiyyar Lafiya wato (STEMM).
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Ministan ilimi na Nijeriya
17 Nuwamba 2025

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kaddamar da shafin neman tallafin jari ga dalibai wato Student Venture Capital Grant (S-VCG) don karfafa wa ƙirƙire-ƙirƙire da dalibai ke jagoranta a faɗin ƙasar.

Matakin na cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Ilimi ta Ƙasar ta fitar a ranar Litinin 17 ga Nuwamban 2025 inda ta ce, gagarumin shirin na daga cikin ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na ware tallafin Naira miliyan 50 ga daliban manyan makarantu a Nijeriya da suka ƙirƙiri wani abu sabo da kasar za ta yi alfahari da shi.

Kazalika, shirin zai taimaka wajen gano da horar da matasa manyan gobe ‘yan Nijeriya tare da samar da hanyar tallafa wa ƙirƙire-ƙirƙirensu masu mahimmaci a fannonin Kimiyya da Fasaha da Injiniyanci da Lissafi da kuma Kimiyyar Lafiya wato (STEMM).

Da yake jawabi a wurin ƙaddamar da shirin, Ministan Ilimi na Nijeriya, Tunji Alausa ya jaddada manufar dabarun shirin inda ya ce "Shugaban Ƙasa ya ƙalubalance mu da mu nemi masu basirar ƙirƙire-ƙirƙire da aka taba yi ba a ƙasar daga cikin manyan makarantunmu.’’

“Ba wai kawai muna neman ayyukan ƙirƙire-ƙirƙire ‘yan Nijeriya ba ne; muna neman ɗaliban jami'o'in Nijeriya waɗanda ayyuakansu za a su zama zakaran gwajin dafi a jami'o'inmu da kwalejojinmu’’ in ji ministan, yana mai cewa, wannan zai zama jari mai ɗumbin riba nan gaba ga Nijeriya."

Ma’aikatar ta bayyana cewa dalibai da suka yi nasara za su samu damar cikakken tsarin tallafin wanda ya haɗa da shirye-shiryen horar da ɗalibai sosai, da jagoranci na ƙwararru daga fannin kasuwanci da na masana'antu, da kuma damar amfani da kayan aiki da suke bukata.

Kazalika daliban za su samu kafa da kuma albarkatun da ake buƙata don haɓaka da kuma faɗaɗa sabbin ƙirƙire-ƙirƙirensu, kamar yadda sanarwar ma’aikatar ta bayyana.

An tsara shirin ne don tabbatar da cewa, ba a tsaya iya tallafa wa ayyukan da aka ƙaddamar da su ba ne, amma a jagorance zuwa matakin da su iya shiga kasuwa.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?