| Hausa
TURKIYYA
4 minti karatu
'Turkiyya za ta duba buƙatun Saudiyya ƙarƙashin yarjejeniyar Makkah yayin da Houthi ke kai hari'
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya ce akwai yiwuwar Saudiyya na da wasu buƙatun soji sakamakon hare-haren baya-bayan nan da ’yan Houthi suka kai, kuma Turkiyya za ta duba waɗannan buƙatu ƙarƙashin yarjejeniyar tsaro ta Makkah.
'Turkiyya za ta duba buƙatun Saudiyya ƙarƙashin yarjejeniyar Makkah yayin da Houthi ke kai hari'
Fidan ya ce Ankara na sa ido sosai a kan lamarin a karkashin tsarin yarjejeniyar tsaro ta Makkah.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya ce akwai yiwuwar Saudiyya na da wasu buƙatun soji sakamakon hare-haren baya-bayan nan da ’yan Houthi suka kai, kuma Turkiyya za ta duba waɗannan buƙatu ƙarƙashin yarjejeniyar tsaro ta Makkah. Ya kuma ce ba zaa amince a jawo Riyadh cikin yaƙin da ke tsakanin Amurka da Iran ba.

Fidan ya ce ana barazana ga mutuncin yankin ƙasar Saudiyya da kuma ikon mallakarta yayin da hare-haren ’yan Houthi ke ci gaba, yana mai jaddada cewa Turkiyya tana tare da Riyadh.

Da yake magana da gidan talabijin na NTV a ranar Asabar, ya ce yanayin da ake ciki a kusa da mashigar ruwa ta Bab al-Mandab na ƙara lalacewa, yayin da illolin tattalin arziƙin da lamarin ke haddasawa suka kai matakin da ba za a iya jurewa ba.

Fidan ya kuma ce Isra’ila na haifar da haɗari ba ga Gabas ta Tsakiya kaɗai ba, har ma ga duniya baki ɗaya.

Fidan ya ce Turkiyya ta yi Allah-wadai da hare-haren, musamman waɗanda aka kai kan wuraren man fetur da kuma birnin Makkah mai tsarki. Ya ƙara da cewa Turkiyya na sa ido sosai kan lamarin ƙarƙashin yarjejeniyar Makkah.

“Ƙawancen Makkah yana mataki mai kyau sosai. Akwai ƙuduri mai ƙarfi da aka bayyana. Muna aiki da dukkan ƙarfinmu domin aiwatar da wannan ƙuduri,” in ji Fidan.

Ya ƙara da cewa: “Ƙawancen Makkah zai kasance wani dandali da zai sauya yanayin abubuwa sosai.”

Ya ce ana gudanar da wasu shirye-shirye da dama domin warware rikicin, amma ya kamata ɓangarorin da abin ya shafa su samar da sakamako na zahiri.

A wani ɓangare kuma, Fidan ya ce ba abin da za a amince da shi ba ne a jawo Saudiyya cikin yaƙin da ke tsakanin Amurka da Iran, yana mai jaddada cewa Riyadh ba ta da muradin shiga cikin rikicin.

Yaƙin Ukraine da Rasha

Fidan ya ce Turkiyya ta aika da shawara ga Kyiv da Moscow da nufin kawo ƙarshen faɗan da ke faruwa a Bahar Maliya, kuma tana jiran amsa daga ɓangarorin biyu.

Ya ce babban abin da ya fi muhimmanci a nan take shi ne sake dawo da jigilar hatsi daga yankin.

Fidan ya ce ana kuma gudanar da wasu manyan shirye-shirye da nufin kawo ƙarshen yaƙin gaba ɗaya, amma ya amince cewa samun mafita mai ɗorewa ga rikicin na da wuya a wannan mataki.

Yarjejeniyar Makkah da Tashin Hankalin Gabas ta Tsakiya

Turkiyya, Saudiyya da Pakistan sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro a wani taron ƙasashen uku da aka gudanar a Makkah a ranar 7 ga Agusta, 2026, inda suka yi alƙawarin ƙarfafa tsaron bai ɗaya, zurfafa haɗin gwiwar tsaro da kuma inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da ma sauran sassan duniya.

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya bayyana yarjejeniyar a matsayin wakilcin “ƙudurin dabarun aiki” domin mayar da martani ga sauye-sauyen yanayin yankin. Ya ƙara da cewa tsarin haɗin gwiwar ƙasashen uku ba martani ba ne ga “abubuwan da ke faruwa yau da kullum”.

Tashin hankalin Gabas ta Tsakiya ya ƙaru bayan da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar da manyan hare-hare kan Iran a watan Fabrairu, lamarin da ya sa Tehran ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan sansanonin Amurka da ke faɗin yankin.

Pakistan ta shiga tsakani domin rage tashin hankalin, inda ta taimaka wajen cim ma yarjejeniya tsakanin Washington da Tehran a watan Yuni domin kawo ƙarshen faɗan da ke tsakaninsu.

Daga baya dai yarjejeniyar ta samu tangarda sakamakon rashin jituwa tsakanin ƙasashen biyu kan mashigar ruwan Hormuz.

Yemen na cikin rikici tun bayan da ’yan Houthi suka ƙwace babban birnin ƙasar, Sana’a, da wasu larduna a watan Satumbar 2014, lamarin da ya sa ƙawancen ƙasashen Larabawa ƙarƙashin jagorancin Saudiyya ya shiga tsakani a watan Maris na 2015 domin mara wa gwamnatin da ƙasashen duniya suka amince da ita baya.