| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Ɗanyen man da Nijeriya ke samarwa ya kai matakin da ya fi yawa tun watan Yunin 2020
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito cewa ƙididdigar da hukumar da ke sa ido a kan fannin haƙo man fetur ranar Lahadian ta ce an samu samu ƙarin ne sakamakon daidaituwar aiki da ingancin bututun mai.
Ɗanyen man da Nijeriya ke samarwa ya kai matakin da ya fi yawa tun watan Yunin 2020
Tsohon Hoto: Matatar mai Dangote na cikin ababe ci-gaban da aka samu a masana'antar man Nijeirya cikin 'yan shekarun nan

Adadin ɗanyen man da Nijeriya ke samarwa ya kai mataki mafi ƙololuwa cikin sama da shekara shida a watan Yuni, inda ya ɗara kason da ƙungiyar OPEC ta ware mata.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito cewa ƙididdigar da hukumar da ke sa ido a kan fannin haƙo man fetur ranar Lahadian ta ce an samu samu ƙarin ne sakamakon daidaituwar aiki da ingancin bututun mai.

Ƙasar da ta fi samar da mai a nahiyar Afirka ta samar da gangar ɗanyen mai miliyan 1.56 a ko wace rana a watan da ya gabata, adadin da ya zarce ganganr mai miliyan 1.5 a ko wace rana da OPEC ta bai wa Nijeriya damar fitarwa.

Kazalika alƙallumna sun nuna cewa ƙasar ta ta cim ma kashi 104 cikin 100 na biyayya ga doka.

Idan aka haɗa da wani nau’in mai (condensates) da ba ya ƙarƙashin ikon kason OPEC, adadin man da Nijeriya ta samar ya kai kimanin gangar mai miliyan 1.735 a ko wace rana a watan Yuni, adadin da baiu wuce gangar mai miliyan 1.700 a ko wace rana ba a watan Mayu.

Reuters ya ruwaito cewa wannan shi ne wata na huɗu a jere da adadin man ke ƙaruwa.

Adadin man da ƙasar ta samar a watan Yuni shi ne adadi mafi yawa da ƙasar ta samar tun watan Afrilun shekarar 2020, adadi mafi yawa cikin watanni 74.

Daidaituwar aiki a wuraren haƙar mai da kuma rashin toshe ko wane muhimmin bututun mai sun taimaka wajen ƙara lokacin haƙar mai da kuma yawan man da ake fitarwa, in ji alƙalluman.

Rumbun Labarai
Kaduna, Sokoto, Zamfara da wasu jihohin Nijeriya 10 na fuskantar barazanar ambaliya - NiMet
‘Yansandan Nijeriya 10 sun rasa rayukansu a musayar wuta da mahara a arewacin ƙasar, in ji hukumomi
'Yan Nijeriya sun kashe Naira tiriliyan 6.6 kan sayen datar waya a cikin shekara ɗaya
Mutane 237 ne suka mutu sakamakon zazzaɓin Lassa a watanni bakwai na 2026 a Nijeriya - NCDC
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu  kwamandojin ISWAP tara a Borno
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu 'carry-over' a jami'a
Super Falcons da Indomitable Lionesses na gogayyar shiga Gasar Kofin Duniya
Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar
Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna
Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa
An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja
An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta'adda
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau