AFIRKA
5 minti karatu
Dangantaka tsakanin Turkiyya da Afirka ta shiga wani sabon babi mai ƙarfi – Kwamishinar Ƙungiyar AU
Jawabin kwamishinar ya nuna karuwar fahimtar juna tsakanin shugabanni cewa wannan kawance ba kawai yana tasowa ba ne, amma yanzu ya tabbata kuma yana sake fasalin yadda kasashen kudancin duniya ke gudanar da kasuwanci.
Dangantaka tsakanin Turkiyya da Afirka ta shiga wani sabon babi mai ƙarfi – Kwamishinar Ƙungiyar AU
Francisca Tatchouop Belobe
17 Oktoba 2025

An kammala taron kasuwanci da tattalin arziki na biyar tsakanin Turkiyya da Afirka (TABEF) a ranar Jumma’a a Istanbul, inda aka kara karfafa daya daga cikin kawance mafi tasiri tsakanin kasashen kudancin duniya.

Taron, wanda aka gudanar karkashin taken “Amfani da Dangantakar Turkiyya da Afirka don Amfanin Juna,” ya tara fiye da mahalarta 4,000, ciki har da shugabannin kasashe, ministoci, jakadun kasashen waje, da shugabannin bangaren masu zaman kansu daga nahiyar Afirka da Turkiyya.

A cikin daya daga cikin jawabai mafi jan hankali a taron, Francisca Tatchouop Belobe, Kwamishinan Kungiyar Tarayyar Afirka mai kula da Ci gaban Tattalin Arziki, Yawon Bude Ido, Kasuwanci, Masana’antu, da Ma’adinai, ta bayyana kawancen Turkiyya da Afirka a matsayin “bai tsaya kan gaskiya ba kawai ba, amma wanda ya yi nisan da ba ya jin kira”.

Jawabinta ya nuna karuwar fahimtar juna tsakanin shugabanni cewa wannan kawance ba kawai yana tasowa ba ne, amma yanzu ya tabbata kuma yana sake fasalin yadda kasashen kudancin duniya ke gudanar da kasuwanci.

‘Abokiyar Amana’

“Turkiyya ba bakuwa ba ce a wannan tafiya,” in ji Kwamishina Belobe. “Abokiyar amana ce, tana gina, zuba jari, sauraro, da aiki tare da burin Afirka.”

Kwamishinar ta bayyana ci gaban tattalin arziki mai ban mamaki a jawabinta. “A cikin shekaru fiye da ashirin kacal, cinikayya tsakanin Afirka da Turkiyya ta karu daga dala biliyan 4.5 a shekarar 2003 zuwa fiye da dala biliyan 40.7 a shekarar 2024,” in ji ta.

Wannan ci gaba mai ban mamaki ya sanya Turkiyya cikin manyan abokan cinikayya guda biyar na ƙasashen da ba na Afirka ba a nahiyar. Tare da burin cim ma dala biliyan 50 nan da shekarar 2026, Belobe ta lura cewa karfin wannan dangantaka ba kawai tana da karfi ba ne, amma tana kara karuwa.

“Muna ganin dangantakar da aka gina bisa ga kudurin siyasa da burin bangaren masu zaman kansu,” in ji ta. “TABEF hujja ce cewa wannan ba kawai diflomasiyya ba ce — amma aiki ne.”

Fiye da Adadin Cinikayya

Zuba jarin Turkiyya a Afirka yana nuna tsanaki da zurfin dangantaka. Zuba Jarin Kai Tsaye na Wajen Turkiyya (FDI) ya zarce dala biliyan 8.5, yana tallafa wa ayyuka a bangarori kamar makamashi mai sabuntawa, dabarun dijital, masana’antu, gine-gine, da sauransu.

Fiye da kamfanoni 1,500 na Turkiyya ke aiki a Afirka, galibi suna yin hadin gwiwa kai tsaye da kananan masana’antu da cibiyoyi na cikin gida.

“Turkiyya tana zuba jari ba don amfani kawai ba, amma don sauyi,” in ji Belobe. “Tana tallafa wa kananan masana’antu, tana raba fasaha, tana samar da kwarewa, wannan shi ne hangen nesa na dogon lokaci a aikace.”

Yawancin wadannan kawance sun bayyana a yankin baje-kolin taron, inda Belobe ta gana da ‘yan kasuwa da masu kirkira daga nahiyar. Ta jaddada wani kamfani na Afirka da ke amfani da fasahar wucin-gadi don sauya dabarun, da wani kamfani na Turkiyya da ke kirkirar hanyoyin makamashi mai dorewa a karkarar Afirka.

“Wadannan ba labarai ne kawai ba. Hujjoji ne,” in ji ta. “Wannan shi ne yadda kawance na karni na 21 yake — kirkira tare da amfanin juna.”

Afirka, ta jaddada, ba kawai tana bude kasuwanci ba ne, amma tana tsara makomar kasuwancin kanta. A shekarar 2024, nahiyar ta jawo dala biliyan 97 na zuba jari kai tsaye, wanda ya wakilci karin kashi 7.5% daga shekarar da ta gabata.

Cinikin cikin Afirka ya karu zuwa dala biliyan 280, kuma kasashe 15 sun samu karuwar ma’aunin GDP na fiye da kashi 5%, duk da kalubalen duniya.

Amfanin Yawan Jama’a na Afirka

Mafi muhimmanci, amfanin yawan jama’a na Afirka yana daya daga cikin manyan kadarorinta. Tare da matsakaicin shekaru na 19.5 kacal da yawan jama’a da ake sa ran zai kai biliyan 2.5 nan da shekarar 2050, nahiyar tana da mafi girman adadin matasa, kirkira, da bukatu a duniya.

“Nan da shekarar 2030, kashi 43% na matasan duniya za su kasance ‘yan Afirka,” in ji Belobe. “Mu ne nahiyar da ta fi kowacce matasa — kuma wadannan matasa su ne kuzari, buri da makoma,” kamar yadda ta bayyana.

Tsarin Cinikayya na Marsa Shinge na Afirka (AfCFTA) - wani muhimmin shiri karkashin Ajandar AU ta 2063, shi ma ya kasance a matsayin ginshikin sauyin tattalin arzikin nahiyar.

Tare da kimanin darajar dala tiriliyan 6.7 nan da shekarar 2035, AfCFTA na shirin zama kasuwar ciniki guda mafi girma a duniya. Belobe ta yaba da goyon bayan Turkiyya ga ajandar cinikayya ta nahiyar, tana mai lura da cewa kudurin Ankara ya wuce yarjejeniyoyin bangarori biyu zuwa tallafa wa hadewar yankuna.

“Turkiyya ta fahimci cewa karfin Afirka yana cikin hadin kanta; gine-ginen iyaka, da dokokin cinikayya masu daidaito,” in ji ta.

TABEF, wanda aka gudanar a Cibiyar Taro ta Istanbul, ya kasance fiye da taron al’ada. Wuri ne da aka tattauna yarjejeniyoyi, aka sanar da kawance, kuma aka tsara bangarori don zuba jari a nan gaba. An tattauna batutuwa daga makamashi maras gurɓata muhalli zuwa kayan aikin dijital, inda ake kallon Turkiyya a matsayin abar dogaro wurin zuba jari.

Rumbun Labarai
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan