| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
“Domin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda ya umarci Malam Yahya ya shirya kare kansa bisa zargin da ake masa a gaban majalisar malamai," in ji sanarwar.
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Malam Yahaya Masussuka
18 Nuwamba 2025

Gwamnatin Jihar Katsina a arewacin Nijeriya ta ce za ta shirya muƙabala tsakanin Sheik Yahya Masussuka da ke da'awar a bi Ƙur’ani zalla da kuma sauran Malaman addinin Musulunci na jihar.

A wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar ya fitar a ranar Talata mai ɗauke da sa hannun daraktan yada labarai, Ibrahim Almu Gafai, ta ce za ta shirya muƙalabar ne bayan da sulhun da Fadar Sarkin Katsina ta yi wa Masussuka da Kungiyar Izala kwanakin baya ya ci tura.

Sanarwar gwamnatin ta ce tun da fari Ƙungiyar Izala ta kai ƙorafi kan cewa Yahya Masussuka abin da yake wa’azi a kai ya ci karo da Shari’ar Musulunci, inda shi ma Masussukan ya kai nasa ƙorafin cewa ‘yan izalar na cin mutuncinsa da barzanar kai masa hari.

Hakan ne ya sa gwamnatin ta yanke hukuncin tura matsalar gaban Sarkin Katsina don a yi musu sulhu, “inda Sarkin ya yanke hukuncin cewa babu wani malami da yake da damar yin wa’azi ko bin wata koyarwa da za ta ɓata ran Musulmai.”

Amma a sanarwar tata ta ranar Talata, gwamnatin Katsinan ta ce har yanzu ba a samu maslaha ba a kan lamarin.

“Domin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda ya umarci Malam Yahya ya shirya kare kansa bisa zargin da ake masa a gaban majalisar malamai.

“Daga nan ne kuma za a tsara dokoki da tsare-tsare wadanda daga sannan duk wanda ya kauce musu to gwamnati za ta dauki matakin da ya dace a kan ko waye,” in ji sanarwar.

A karshe gwamnatin ta umarci al’umma da su yi hakuri saboda za a yi adalci a kan mas’alar.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?