| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Mai Bai wa Trump Shawara kan Addini tana shan raddi bayan ta kwatanta shi da Yesu Almasihu
Mai ba da shawara kan lamuran addini ta Shugaban Amurka Donald Trump tana fuskantar suka daga ko’ina a kafofin sada zumunta bayan ta kwatanta Trump da Yesu Almasihu a ranar Laraba.
Mai Bai wa Trump Shawara kan Addini tana shan raddi bayan ta kwatanta shi da Yesu Almasihu
Kalaman Paula White-Cain game da Donald Trump sun haifar da zargin sabo a tsakanin masu suka a shafukan yanar gizo. / AFP

Ana ci gaba da mayar da kakkausan martani a kafofin sada zumunta ga Mai Bai wa Trump Shawara kan Addini Paula White-Cain bayan ta kwatanta gwagwarmayar da Shugaba Donald Trump da na Yesu Almasihu (Annabi Isa AS) a wasu kalamai masu cike da ce-ce-ku-ce.

Mai ba da shawara kan lamuran addini ta Shugaban Amurka Donald Trump tana fuskantar suka daga ko’ina a kafofin sada zumunta bayan ta kwatanta Trump da Yesu Almasihu a ranar Laraba.

“Yesu ya koyar da darussa da dama ta hanyar mutuwarsa, binne shi, da kuma tashinsa. Ya nuna mana cewa kyakkyawan jagoranci da babban sauyi suna bukatar gagarumar sadaukarwa,” in ji Paula White-Cain.

“Kuma ya kai Shugaba Kasa, babu wanda ya sha wuya kamar yadda ka sha. Kusan hakan ya kusa yin sanadiyyar rayuwarka.

“An ci amanarka, an kama ka, kuma an yi maka kazafi. Wannan tsari ne da Jagoranmu kuma Mai Cetonmu ya nuna mana,” in ji ta.

“Amma hakan bai tsaya a nan ba a gare shi, kuma bai tsaya a nan ba a gare ka kaima.

“A ko da yaushe Allah yana da tsari. A rana ta uku, ya tashi, ya yi nasara a kan azzalumai, ya yi nasara a kan mutuwa da wuta da kuma kabari. Kuma saboda ya tashi, dukanmu mun san cewa za mu iya tashi. Kuma yallabai, saboda tashinsa daga matattu, kai ma ka sake mikewa,” in ji ta.

“Kuma na yi amanna cewa Ubangiji ya ce na gaya maka wannan — saboda nasararsa, kai ma za ka yi nasara a duk abin da ka sa hannunka,” kamar yadda ta shaida wa Trump.

Biyo bayan wadannan kalamai na nata, ma’abota shafukan sada zumunta sun yi wa Cain-White raddi mai zafi, inda wasu suka bayyana jawabin nata da “babban sabo” da kuma “rashin hankali.”

Rumbun Labarai
UAE ta fita daga Ƙungiyar Ƙasashe Masu Arzikin Fetur ta Duniya, OPEC
Waye zai zama Sakatare Janar na MDD? Macky Sall na fuskantar abokan takara daga Latin Amurka
Abubuwan da muka sani game da harbe-harben da aka yi a taron liyafar Trump da manema labarai
Trump ya ce harbin da aka yi ba zai hana shi samun nasara a yakin Iran ba
An fitar da Trump daga wajen liyafa da 'yanjarida yayin da 'wata kara' ta haifar da fargabar tsaro
Gagarumar gobara ta laƙume gidaje 1,000 a ƙauyen da ke kan ruwa, tare da raba dubbai da muhallansu
'Gigitaccen mahaukaci': Sanatocin Amurka sun caccaki barazanar Trump ga Iran a matsayin laifin yaƙi
Trump: Za a kai wa tashoshin lantarki da gadojin Iran hari idan ba a buɗe Mashigar Hormuz ba
Damuwar 'yan Republican na ƙaruwa gabanin zaɓukan rabin wa'adi saboda tasirin yaƙin Iran
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba