| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Nijeriya ta yi gargaɗi kan haɗarin kamuwa da sanƙarau a wasu jihohin arewacin ƙasar
Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya ta bayyana Sokoto, Zamfara, Kebbi, Katsina, Kano, Jigawa, Adamawa, Gombe, Bauchi, Yobe da Borno a matsayin jihohin da ke cikin babban haɗari na kamuwa da cutar.
Nijeriya ta yi gargaɗi kan haɗarin kamuwa da sanƙarau a wasu jihohin arewacin ƙasar
Zazzaɓi mai zafi da ciwon kai da amai ko wuya ya yi tauri na cikin alamomin cutar. / Reuters
11 awanni baya

Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta fitar da sanarwar gargaɗi game da lafiyar jama'a inda ta ce akwai jihohin arewacin ƙasar da dama da ke fuskantar ƙarin haɗarin kamuwa da cutar sankarau yayin da yanayin zafi ke ƙaruwa a sassan ƙasar.

A cikin wata sanarwa, hukumar ta bayyana cewa cutar sanƙarau wata mummunar cuta ce da ke shafar ƙwayoyin kariya da ke rufe ƙwaƙwalwa da lakar baya, kuma galibi ƙwayar cutar Neisseria meningitidis ce ke haddasa ta.

NiMet ta kuma bayyana cewa cutar na yaɗuwa ta hanyar numfashi daga mutum zuwa mutum, musamman a wuraren da ake cunkoso ko kuma wuraren da iska ba ta shiga yadda ya kamata.

Hukumar ta bayyana Sokoto, Zamfara, Kebbi, Katsina, Kano, Jigawa, Adamawa, Gombe, Bauchi, Yobe da Borno a matsayin jihohin da ke cikin babban haɗari na kamuwa da cutar.

Ta kuma buƙaci mazauna yankunan tsakiyar ƙasar da su kasance cikin lura da alamun cutar tare da kai rahoton duk wani zargi kan alamomin cutar da wuri. A halin yanzu, Jihohin Filato, Oyo, Cross River, Edo, Ekiti da Enugu an sanya su cikin yankunan da ba sa ido sosai a kansu.

 “Ku kasance kuna da bayanai. Ku bi shawarwarin hukumomin lafiya kuma ku shiga cikin shirye-shiryen wayar da kan al’umma,” in ji hukumar.

“Ku kare kanku da al’ummarku. Samun bayani da wuri, yin rigakafi, da samun magani da wuri na iya ceton rayuka,” kamar yadda ta ƙara da cewa.

Hukumar ta kuma bayyana cewa duk da cewa cutar na iya tsananta cikin sauri har ta zama barazana ga rayuwa cikin ‘yan sa’o’i idan ba a yi magani ba, gano cutar da wuri da kuma ba da maganin rigakafin ƙwayoyin cutar na iya ƙara yiwuwar a rayu da kuma rage matsalolin da ka iya biyo baya.

NiMet ta ce rukunin waɗanda suka fi fuskantar haɗari sun haɗa da yara da matasa da mutanen da ke rayuwa a wuraren da ke da cunkoso da waɗanda ke fuskantar yanayin zafi da ƙura, da kuma mutanen da garkuwar jikinsu ba ta da ƙarfi.

Alamomin cutar da ya kamata a lura da su sun haɗa da zazzabi mai tsanani da ke zuwa kwatsam da matsanancin ciwon kai, ko wuya ya yi tauri da tashin zuciya ko amai da jin haske yana damun ido.