Gwamnatin jihar Legas a kudu maso yammacin Nijeriya ta kama mabarata 396 kuma ta fara tantance su da zummar mayar da su jihohin da suka fito.
Kwamishinan Muhalli da Albarkatun Ruwa na jihar, Tokunbo Wahab ne ya bayyana hakan a shafinsa na X ranar Talata.
Gwamnatin ta ce waɗanda aka kama ɗin za su samu tallafin da ya dace idan akwai buƙatar hakan kafin a miƙa su ga hukumomin da suka dace domin mayar da su cikin aminci.
Kwamishinan ya ƙara da cewa jami’an rundunar tsaftace muhalli ta jihar Legas (LAGESC) ne suka yi kamen a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnati na tsaftace jihar da kuma daƙile yin ba daidai ba.
Ya ƙara da cewa aikin wata alama ce ta ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na magance matsalar bara a kan tituna da sauran harkokin da ta ke ganin suna zagon ƙasa ne ga tsafatace muhalli da kuma doka da oda.
Sanarwar ta da kwamishinan ya fitar tana tare ne da wani bidiyo da ke nuna gomman waɗanda aka kama ciki har da maza da mata da ƙananan yara da ma masu nakasa.









