| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Jihar Legas ta kama mabarata 396, tana tantance bayanansu domin mayar da su jihohinsu na asali
Gwamnatin jihar ta ce waɗanda aka kama ɗin za su samu tallafin da ya dace idan akwai buƙatar hakan kafin a miƙa su ga hukumomin da suka dace domin mayar da su jihohinsu na asali cikin aminci.
Jihar Legas ta kama mabarata 396, tana tantance bayanansu domin mayar da su jihohinsu na asali
Kwamishinan Muhalli na jihar Legas, Tokumbo Wahab

Gwamnatin jihar Legas a kudu maso yammacin Nijeriya ta kama mabarata 396 kuma ta fara tantance su da zummar mayar da su jihohin da suka fito.

Kwamishinan Muhalli da Albarkatun Ruwa na jihar, Tokunbo Wahab ne ya bayyana hakan a shafinsa na X ranar Talata.

Gwamnatin ta ce waɗanda aka kama ɗin za su samu tallafin da ya dace idan akwai buƙatar hakan kafin a miƙa su ga hukumomin da suka dace domin mayar da su cikin aminci.

Kwamishinan ya ƙara da cewa jami’an rundunar tsaftace muhalli ta jihar Legas (LAGESC) ne suka yi kamen a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnati na tsaftace jihar da kuma daƙile yin ba daidai ba.

Ya ƙara da cewa aikin wata alama ce ta ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na magance matsalar bara a kan tituna da sauran harkokin da ta ke ganin suna zagon ƙasa ne ga tsafatace muhalli da kuma doka da oda.

Sanarwar ta da kwamishinan ya fitar tana tare ne da wani bidiyo da ke nuna gomman waɗanda aka kama ciki har da maza da mata da ƙananan yara da ma masu nakasa.

Rumbun Labarai
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu  kwamandojin ISWAP tara a Borno
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu 'carry-over' a jami'a
Super Falcons da Indomitable Lionesses na gogayyar shiga Gasar Kofin Duniya
Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar
Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna
Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa
An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja
An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta'adda
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro
'Yansandan InterPol sun tasa ƙeyar ɗan China daga Nijeriya kan safarar namun daji