Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba

Matakin na zuwa ne kwanaki bayan dakarun Somaliya sun karɓe iko da babban birnin jihar, lamarin da ya sa shugaban yankin Abdiaziz Hassan Mohamed Laftagaren ya ajiye aiki.

By
Ana tsammanin Jibril Abdirashid Haji Abdi ya jagoranci yankin na riƙon ƙwarya zuwa lokacin da aka yi zaɓe. / Others / Others

Firaministan Somaliya ya naɗa mataimakinsa ya jagoranci jihar Kudu Maso yammacin ƙasar ranar Laraba bayan ajiye aikin shugaban yankin Abdiaziz Hassan Mohamed Laftagaren.

Firaminista Hamza Abdi Barre ya naɗa Jibril Abdirashid Haji Abdi, mataimakin firaminista na biyu, a matsayin shugaban riƙon ƙwarya na yankin.

“Firaministan na gwamnatin tarayyar Somaliya, Mista Hamza Abdi Barre, a wata sanarwa da ya fitar, ya naɗa Mista Jibril Abdirashid Haji Abdi a matsayin shugaban riƙon ƙwarya na jihar Kudu maso yammacin Somaliya,” kamar yadda wani mai magana da yawun gwamnati ya bayyana.

Naɗin na zuwa ne kwanaki bayan dakarun tarayyar Somalia, da goyon bayan dakarun yankin, sun karɓe iko gaba ɗaya da babban birnin jihar, Baidoa, lamarin da ya sa Laftagaren ya ajiye aikin bayan kusan shekara takwas a bakin aiki.

Gwamnatin jihar Kudu maso yammacin ƙasar da kuma ta gwamnatin tarayya a Mogadishu sun kasance cikin rashin jituwa game da mulkin Laftagaren kuma majalisar dokokin tarayyar ƙasar ta amince da garambawul na tsarin mulki game da batun.

Baidoa, wani muhimmin birni mai tattalin arziki da yawa kimanin kilomita 246 (mil 152) kudu maso yammacin Mogadishu, na da ofisoshin Ƙungiyar Tarayyar Afirka da na Majalisar Ɗinkin Duniya (MƊD).

Manyan jami’an gwamnatin tarayya, ciki har da shugaban majalisar dokoki Adan Mohamed Nur Madobe, da ministan harkokin waje Abdisalam Abdi Ali da ministan addini Mukhtar Robow, suna Baidoa domin sa ido kan sauyin na siyasa.