| Hausa
Ra'ayi
GABAS TA TSAKIYA
14 minti karatu
‘Isra’ila ta yi niyyar kashe kowa’: Harin da Amurka ta boye, kuma ba a taba bayyana shi ba
A kusan tsawon shekaru 60, Washington na kawar da kai daga harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan Amurka na USS Liberty. Sai dai kuma, tare da rikicin Gabas ta Tsakiya da ake yi da durkushewar manyan kafafen watsa labarai, shirun na rushewa.
‘Isra’ila ta yi niyyar kashe kowa’: Harin da Amurka ta boye, kuma ba a taba bayyana shi ba
Shekaru sittin lokaci ne mai tsawo don a manta da duk wani lamari. / TRT Russian / TRT World

Kusan shekaru sittin da suka gabata, wani lamari mai ban mamaki ya faru, wanda har yanzu ba a iya warware shi ba.

Yana da matukar tayar da hankali musamman saboda Isra'ila ce mai laifi kuma Amurka, wacce ke daukar Isra'ila a matsayin abokiyar kawance, ita ce wacce abin ya shafa. Duk lokacin da wani ya tuna da wannan lamari, musamman a cikin wata muryar zargi, nan take ana yi musu lakabi da "masu adawa da Yahudawa" ta hanyar amfani da mafi yawancin kafofin watsa labarai.

Duk da haka, yakin da ake yi da Iran, zubar da jini a Gaza da hare-haren da aka kai kan Lebanon sun nuna cewa tasirin kafofin watsa labarai masu goyon bayan Isra'ila kan ra'ayoyin jama'a ba ya tasiri kamar yadda yake a da.

A wannan yanayin, a ranar 8 ga Yunin 2026, dan majalisa Thomas Massie, wanda ya dade yana adawa da taken "Israel First" na jam'iyyar Republican, ya yi amfani da zauren majalisar don dawo da labarin da jami'an Amurka suka fi so su yi watsi da shi tun 1967: harin Isra'ila kan jirgin ruwan USS Liberty, wanda ya kashe ma'aikatan jirgin ruwa 34 kuma, a cewar masu sukar bayanan hukuma, an kai harin ne da gangan.

Shekaru sittin lokaci ne mai tsawo don a manta da duk wani lamari. Ko kuma, mafi daidai, a rufe shi ma baki daya.

Jawabin Massie ya ba da dama ta sake duba abin da ya faru a wannan rana ta bazara a shekarar 1967, da kuma dalilin da ya sa gaskiyar waɗannan abubuwan suka kasance ba su dace da Washington ba, musamman ma a yau, kuma ba su da kyau ga Tel Aviv.

'Kada ku kunyata abokin mu’amalarku'

Jirgin ruwan leƙen asiri na Amurka USS Liberty ya kasance wani ɓangare na shirin leƙen asiri a zamanance na Rundunar Sojan Ruwa ta Amurka da hukumar tsaro ta kasa NSA.

A watan Mayun shekarar 1967, an tura jirgin cikin gaggawa zuwa Gabashin Bahar Rum don sa ido kan Yaƙin Kwanaki Shida da ke tafe. Kasancewar sa a yankin rikici ya sanya shi zama muhimmiyar kadarar leƙen asiri ta Amurka.

A ranar 8 ga Yunin 1967, a lokacin da yaƙin ya yi zafi, jiragen saman Isra'ila da jiragen ruwa na torpedo sun kai hari kan wani jirgin ruwan Amurka a tekun kasa da kasa a yankin Sinai. Cikin sama da awanni biyu kacal, matuƙan jirgin ruwa 34 sun mutu, wasu 170 ko 171 sun ji raunuka daban-daban.

Dangane da yawan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata a tsakanin ma'aikatan jirgin, wannan shi ne daya daga cikin hare-haren da suka fi muni da aka kai wa wani jirgin ruwan yaki na Amurka tun bayan yakin duniya na biyu - kuma daya daga cikin hare-haren da aka fi yin shiru a tarihin dangantakar Amurka da Isra'ila.

Jerin abubuwan da suka faru a wannan ranaba su yi kama da wani abu na arashi ba. Tun daga safiyar ranar, jiragen saman Isra'ila sun yi ta shwagi a saman jirgin a wurare masu nisa.

Yanayin a yankin da aka kai harin na da kyau, krara ana iya ganin lambar jelar jirgin ruwan na Liberty (GTR-5), kuma tutar Amurka tana kadawa a kan jirgin.

Harin jirgin sama na farko ya faru ne da karfe 1:58 na rana agogon yankin - kusan awanni takwas bayan fara sa ido. Jiragen yakin Mirage III sun fara kai harin da wani hari mai kaifi, suna harba bindigogi masu karfin 30mm a kan babban jirgin.

'Yan mintuna bayan haka, jirgin saman Super Mystere ya shiga harin, yana jefa tankunan napalm kuma yana harba nakiyoyi kan jirgin. Hare-haren sun lalata yawancin bindigogin kuma lalata eriyoyinsa.

Jiragen ruwan torpedo sun kai hari daga baya, inda suka ratsa ta gefen kusa da sassan bincike. Lokacin da wadanda suka tsira suka fara hawa jiragen ceton rai, an harba su bam su ma.

Martanin Washington abin mamaki ne. Jiragen sama daga babban jirgin ruwa mai daukar sama na Saratoga , wanda ya yi gaggawar taimakawa, an dawo da su bisa umarnin Sakataren Tsaro McNamara kai tsaye - kuma, a cewar rahotanni, tare da amincewar Shugaba Johnson, wanda aka rawaito ya ce ba shi da niyyar "kunyata abokin tarayya."

Gangamin diflomasiyya da farfaganda a kafofin watsa labarai ya fara bayyana. Isra'ila ta nemi hana wata badakala ta ƙasa da ƙasa, yayin da Amurkawa ke neman takaita tasirin siyasa a cikin gida.

Sakamakon haka, an sassauta labarin abubuwan da suka faru a bainar jama'a kuma an gabatar da shi cikin sauri a matsayin "kuskure." Isra'ila ta yi iƙirarin cewa matukan jirgin sun yi kuskuren ɗaukar jirgin saman Masar a matsayin na Liberty.

Washington ta karɓi waɗannan bayanai ba tare da wata tirjiya ba. An kira kwamitin bincike na jiragen ruwa cikin gaggawa a tashar jiragen ruwa da ke Malta, inda aka sanya jirgin da ya lalace a kan hanya, kuma ta kammala aikinta da sauri - da alama ba tare da yin tambayoyi masu bayyana gaskiyar lamarin ba.

Majalisar Dokoki ba ta gudanar da bincike mai zaman kansa ba, kuma an hana ma’aikatan da suka tsira tattauna batun inda ake musu baraznaar gurfanarwa a gaban kotu.

Duk da haka, Isra'ila ba ta taɓa ja da baya daga matsayinta ba, kuma an ja biyan diyya ya dauki tsawon shekaru.

Niyya da makirci

Mayaka a jirgin ruwan Liberty sun yi sintiri a tekunan El Arish da ke gabar Masar, wani yanki da aka rawaito cewa sojojin Isra'ila sun yi kisan gilla ga fursunonin yaƙi na Masar da Falasɗinu.

A lokaci guda, jirgin ruwan yana da ikon katse hanyoyin sadarwa na rundunar sojojin Isra'ila, gami da shirye-shiryen mamaye Tuddan Golan - wani aiki da ake kyautata zaton gwamnatin Isra'ila ta ɓoye daga Washington.

Mai bincike James Bamford ya rubuta a cikin littafinsa: shugabannin Isra'ila sun fara ɓoye Yaƙin Kwanaki Shida a bayan wani shinge da aka gina da kyau na yaudara - daga sarrafa barazanar Masar zuwa ƙarya kai tsaye ga Majalisar Dinkin Duniya da shugaban Amurka.

A 2017, mujallar Rundunar Sojojin Ruwa ta Amurka ta buga shaidar cewa, a cikin wata hira a shekarun 1970, Sakataren Harkokin Wajen Amurka Dean Rusk ya yarda cewa harin da aka kai kan Liberty "ba hatsari ba ne, amma aiki ne da gangan."

A shekarar 1977, CIA ta fitar da rahotannin leƙen asiri guda uku, tun daga shekarar 1967, ga jama'a a ƙarƙashin Dokar 'Yancin Bayanai.

Da yake ambaton majiyoyin leƙen asiri a Tel Aviv, takardun sun yi iƙirarin cewa sojojin Isra'ila sun san tutar USS Liberty kuma Ministan Tsaro Moshe Dayan da kansa ne ya ba da umarnin kai harin.

A cewar ɗaya daga cikin waɗannan rahotannin leƙen asiri, wani matukin jirgin Isra'ila ya kai rahoto ga ofishin kwamandan cewa yana kallon wani jirgin yaƙi na Amurka kuma an kama shi bayan ya ƙi aiwatar da umarnin lalata jirgin.

Buga waɗannan takardu a jaridu ya haifar da babban abin kunya. Duk da haka, a wannan shekarar, a ABC, Daraktan CIA Stansfield Turner ya yi watsi da waɗannan rahotannin a matsayin "bayanan sirri" - wato, bayanan da ba a tabbatar da su ba daga masu ba da labari.

Terner ya jaddada cewa rahoton bincike na ƙarshe na hukumar, wanda aka tattara bayan tantance duk bayanan da ake da su, ya kai nuna akasin haka: shugabannin Isra'ila ba su da niyyar kai hari kan jirgin ruwan Amurka.

A shekara ta 2003, hukumar NSA, a matsayin wani ɓangare na ƙarar Dokar 'Yancin Samun Bayanai, ta bayyana sirrinta kuma ta miƙa wa masu bincike bayanan sauti da takardun tattaunawa game da harin bam ɗin kan Liberty.

Amma ko a nan ma, kamar yadda ya bayyana, ba komai ne yake lafiya ba - kayan da aka bayyana ba su da cikakkun bayanai masu mahimmanci, kuma an cire ko share sassan da suka dace na takardun.

A bikin cika shekaru 40 da bala'in, NSA ta sanar da cewa ta kammala bitar duk sauran bayanan kuma za ta buga su gaba ɗaya. Duk da haka, a 2017, kafar The Intercept, ta rawaito cewa bisa ga takardu daga bayanan Snowden, wasu bayanai game da harin har yanzu suna cikin sirri.

Daga cikin takardu da Fadar White House ta shafe shekaru tana ƙoƙarin ɓoyewa a ƙarƙashin "babban sirri", lambar sadarwa ta 0854 tana da matsayi mai muhimmanci. An aika ta ne daga ofishin Jami'in Tsaro na Amurka da ke Tel Aviv kwana biyu kacal bayan kisan kiyashin.

A cewar wannan takarda, Washington ta mallaki shaidu kai tsaye tun daga farko: matukan jirgin Isra'ila, ƙarƙashin umarnin rundunar ƙasa, sun yi aƙalla bincike sau biyu, sun gano tutar Amurka a fili a kan USS Liberty, kuma sun ba da rahoton hakan sau biyu.

Sai bayan da hedikwatar ta tabbatar da cewa jirgin da ke gabansu jirgin ruwan Amurka ne kawai aka ba matukan jirgin umarni na biyu na buɗe wuta.

Wannan makircin na yin shiru ya haɗa da rahoton Kwamitin Raba Kuɗi na Majalisar Wakilai (HAC), wanda NSA ta ƙi bayyana wa jama'a bisa dalilai na shari'a.

A cewar shaidar tsaffin masu sharhi na CIA da mambobin Majalisar Wakilai, takardar ta ɓoye gaskiyar da ba ta dace ba: tun a ranar 7 ga Yunin 1967, kwana ɗaya kafin harin, Isra'ilawa sun yi barazanar lalata USS Liberty ko dai ia janye jirgin leƙen asiri nan da nan daga ruwan ƙasashen duniya a bakin tekun Sinai.

‘Abin kunya’

Sirrin da ke tattare da lamarin ya daɗe tsawon shekaru da dama. Matuƙan jirgin ruwa da suka tsira sun yi ta ikirarin cewa bayan dawowar su, an hana su tattauna harin a bainar jama'a, a ƙarƙashin barazanar ɗaukar matakin ladabtarwa.

Daya daga cikin jami'an ya tuna cewa babban jami’in sojin ruwa ya kira shi zuwa wani ofis a rufe, ya cire masa alamar mukaminsa, ya nemi cikakken bayani game da abin da ya gani, kuma ya yi gargaɗin cewa idan ya gaya wa wani, zai fuskanci ɗaurin kurkuku.

A shekara ta 2003, Kyaftin Ward Boston, babban lauya ga hukumar sojin ruwa da ta binciki harin na 1967, ya ba da shaida a ƙarar Dokar 'Yancin Samun Bayanai game da matsin lamba.

A cikin rantsuwar da ya yi, ya yi ƙirarin cewa Shugaba Lyndon Johnson da Sakataren Tsaro Robert McNamara sun ba da umarnin gano "kuskuren asali," duk da abin da ya ce shaida ce akasin haka.

Boston ta danganta shirun da ya yi na tsawon shekaru da horon soja: "Lokacin da umarni suka zo, ina aiwatar da su." Ya yanke shawarar yin magana bayan buga wani littafi da ke kare sigar hukuma kuma, a ganinsa, ya ɓata gaskiyar batun.

Tsohon Shugaban Hafsoshin Sojan Sama, Admiral Thomas Moorer, wanda ya shiga cikin binciken lamarin, ya kira shi "gargajiyar ɓoye bayanai ta Amurka."

Ya ce ba ya shakkar cewa hari ne da aka kai da gangan. Ya bayyana kiran jiragen ceto a matsayin "abin kunya mafi muni" da ya gani a aikinsa na soja. Moorer ya kuma yi tambaya kan dalilin da ya sa hukumomin Amurka za su iya fifita muradun Isra'ila fiye da muradun ƙasarsu.

A watan Janairun 2024, a lokacin zaman sauraren ƙara a kan HB 1041 a Majalisar Wakilai ta New Hampshire, an ba wa tsoffin sojojin USS Liberty damar gabatar da labarin abubuwan da suka faru ga hukumar gwamnati a karon farko cikin shekaru da dama.

Dokar za ta kafa kwamiti na musamman don bincika harin 1967 da kuma abin da ya biyo baya.

Da yake jawabi a gaban Kwamitin Majalisar Dokoki kan Hulɗar Kasa da Tarayya da Harkokin Tsoffin Sojoji, Larry Bowen, wanda ya karɓi kambin Purple Heart, ya ce gwamnatin Amurka ta gaza taimaka wa ma'aikatan jirgin kuma daga baya ta hana waɗanda suka tsira daga tattauna lamarin a bainar jama'a. A cewar tsohon soja, shaidar ma'aikatan jirgin da sakamakon binciken an tsara su ne don su dace da labarin Isra'ila.

Bowen ya lura da cewa: "Ban taɓa samun damar gaya wa jama'ar Amurka abin da ya faru ba. Gwamnatinmu ba ta zo mana da taimako ba. Ta rufe mana baki, ta hana mu magana game da lamarin kuma ta yi mana barazanar ɗaurin kurkuku da tara idan muka keta wannan haramcin.

"Gwamnatinmu ta gaza gudanar da cikakken bincike kan harin. Rundunar Sojan Ruwa ta kira wani kwamiti na bincike kuma ta sami shaida daga wasu daga cikin abokan aikina, amma daga baya aka umarce su da su daidaita wannan shaidar don ta dace da labarin kuskuren asalin da Isra'ila ta gabatar a cikin neman afuwa kan harin."

Rikicin bayar da labarin

Ko da yake ba kasafai ake tada wannan batu a kafafen watsa labarai ba kuma ana ganin ba a so, 'yan siyasa da manyan mutane daban-daban suna komawa kan lamarin lokaci-lokaci. Misali, a ranar tunawa da lamarin—8 ga Yuni, 2026—Dan Majalisar Wakilai na Jam'iyyar Republican Thomas Massie ya gabatar da jawabi a Majalisar Wakilai, inda ya kira harin "ba tare da wani dalili ba" kuma ya bukaci a sake yin wani bincike.

Mambobi goma sha biyu da suka tsira daga cikin ma'aikatan Liberty, wadanda yawancinsu suka haura shekara tamanin, sun zauna a cikin gidan tarihin da suka ziyarta.

Dan Majalisar Wakilai na Kentucky, wanda kwanan nan ya sha kaye a zaben fidda gwani inda kungiyoyin masu goyon bayan Isra'ila suka yi masa yakin neman zabe da kuma zuba jari mai yawa a cikin manufarsa, ya bayyana cewa: "Bari mu gudanar da bincike. Bari mu zartar da kuduri da zai girmama su. An daɗe ana jira."

A jawabinsa, ya tuna cewa ganin wannan rana ya yi daidai, tutar Amurka a bayyane take, kuma jiragen saman Isra'ila suna zagayawa a kan jirgin a ranar da ta gabaci ta kai harn.

"Isra'ilawa ba su yi niyyar barin wani ya tsira ba," in ji shi, yana mai bayyana harin sama na mintuna 25 da aka kai. Domin ya goyi bayan matsayinsa, Massey ya ambaci 'yan siyasa da jami'an soji da aka ambata a baya, ciki har da Rusk da Moorer:

"Babu ɗaya daga cikin waɗannan mutane masu daraja da ya yarda cewa wannan kuskure ne," in ji ɗan majalisar. "Suna da yakinin cewa wannan kisan gilla ne da gangan - ko dai aikin kokarin boye ƙarya ko yunƙurin ɓoye abin da Isra'ila ke yi a wannan rana."

Magoya bayan labarin mahukuntan Isra'ila, ba shakka, sun ƙi yin zargin cewa an kai harin da gangan.

JNS mai goyon bayan Isra'ila da sauran kafafen watsa labarai irin ta sun bayyana jawabin Massie a matsayin "haɓaka ka'idojin makirci", yayin da ɗan'uwan ɗan siyasar Isra'ila Dan Crenshaw ya nuna cewa kawai yana neman masu sauraro a kafofin watsa labarai masu adawa da Isra'ila don amfanin kansa ne.

Mutane da yawa suna ci gaba da danganta lamarin da "lalacewar kurakurai" a yaƙi. A cikin wannan tsari, ba a nuna harin a matsayin harbin ma'aikatan jirgin ruwa na Amurka ba amma a matsayin wani lamari na "abokantaka" na yau da kullum, wanda ya haifar da rudanin sadarwa, gajiyar matukan jirgi, da gazawar manyan tsare-tsare a tsarin sadarwa a ɓangarorin Isra'ila da Amurka.

Hakazalika, masu goyon bayan wata fassarar daban game da lamarin an mayar da su zuwa ga rukunin wasu mutane da ake yi musu taken "Ku tuna da 'Yanci" ya zama wani ɓangare na ra'ayin cewa "Isra'ila muguwa ce."

A bara, Candace Owens, tsohuwar mai fafutukar kare Isra'ila wacce ta yi aiki a kafafen watsa labarai na Amurka na Yahudawa, ta yi hira da daya daga cikin wadanda suka tsira daga harin kuma ta ce, "Babu wani labari da ya fi bayyana irin yaudara da mummunan halin Isra'ila ta zamani da tasirinta ga gwamnatin Amurka."

Duk wata shaida daga tsoffin sojojin ruwa da suka tsira, kalamai daga manyan jami'an Pentagon, ko bincike mai zaman kansa da ke nuna yanayin harin da gangan, ba a yi watsi da shi ba a cikin wannan tattaunawar.

Ba a tabbatar da cikakken hoton lamarin da ya faru shekaru sittin da suka gabata ba, kawai saboda ba a yi wani kokari na sake fito da shi ba.

Kawance da aka yi na tsawon shekaru a rumbunan bayanai na gwamnati ya ci gaba. Hukumomin leken asiri ba sa son bayyana takardun, domin bayyana su a bainar jama'a zai kawar da tatsuniyar da ake yi ta harin na bisa "kuskure ba da gangan ba."

Duk da haka, a kan asalin yakin da ake yi a Gabas ta Tsakiya, zarge-zargen da ake yi wa Isra'ila da kuma bukatar a gudanar da bincike wanda Washington ta dade tana kokarin binnewa, tare da matuƙan jirgin ruwa da suka mutu, suna ƙara ƙarfi.