GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Makamai masu linzamin Iran sun lalata gini da haddasa gobara a Isra’ila
Hukumomi a Isra'ila sun ce wani ginin da ake zama a ciki ya lalace bayan wani makami mai linzami ya sauka a cikinsa.
Makamai masu linzamin Iran sun lalata gini da haddasa gobara a Isra’ila
Daga Tubas an hango makamai masu linzami da aka harba daga Iran zuwa Isra’ila
18 Yuni 2025

Makamai masu linzami na Iran sun faɗa a wasu wurare a Isra’ila, lamarin da ya janyo gobara tare da lalata wani gini bayan tsarin tsaron saman Isra’ila ya kasa tare harin.

Wasu makamai masu linzamin da aka yi imanin cewa an harbo su ne daga Iran sun sauka a cikin Isra’ila, in ji gidan rediyon rundunar sojin Isra’ila.

Duk da cewa rundunar sojin ba ta bayyana haƙiƙanin inda makaman suka sauka ba, jaridar Israel Hayom Daily ta ba da rahoton cewa aƙalla makamai masu linzami biyu sun faɗi a kusa da Birnin Ƙudus da kuma yankin Sharon kusa da Tel Aviv bisa nazari na farko-farko.

Kafar Channel 12 ta ba da rahoton cewa harin na makamai masu linzami ya lalata wani gini a tsakiyar Isra’ila kuma ‘yan kwana-kwana sun amsa kira [na zuwa inda] motoci 20 suka kama da wuta.

Rahotanni sun ce tarkacen makamai masu linzami sun sauka a wani gini a arewacin Isra’ila, yayin da makamai masu linzami da ke faɗowa da burbuɗinsu sun janyo gobara a fili a wurare da dama.

Tun ranar Juma’a ne dai tashin hankali ya yi ƙamari a yankin yayin da Isra’ila ta ƙaddamar da hare-haren sama a faɗin Iran, ciki har da sansanonin soji da na nukiliya, lamarin da ya sa Tehran ta ƙaddamar da hare-haren ramuwar gayya.

Hukumomin Isra’ila sun ce aƙalla mutum 24 ne aka kashe yayin da ɗaruruwa suka ji rauni tun wancan lokacin a hare-haren makamai masu linzamin Iran.

Iran ta ce aƙalla mutum 224 ne aka kashe inda sama da mutum 1,000 suka ji rauni a harin Isra’ila.

 

Rumbun Labarai
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana
Cikin hotuna: Falasdinu ta cika shekara ta biyu ta kisan ƙare-dangi na Israila a Gaza