NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan ƙaruwar talauci a Nijeriya
“Dole a yi taka-tsan-tsan wajen fassara alƙaluman Bankin Duniya kai-tsaye,” in ji Sunday Dare, mai bai wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan watsa labarai.
Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan ƙaruwar talauci a Nijeriya
Shugaba Bola Tinubu na Nijeriya
9 Oktoba 2025

Gwamnatin Nijeriya ta musanta rahoton da Bankin Duniya ya fitar wanda ya yi ƙiyasin cewa ‘yan ƙasar miliyan 139 suna rayuwa cikin talauci, tana mai cewa ya ci karo da hankali kuma ya saɓa wa yanayin tattalin arzikin ƙasar.

Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan watsa labarai, Sunday Dare, ya bayyana a wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba cewa ƙididdigar da Bankin ya yi amfani da ita wajen fitar da rahoton ba ta yi la’akari da wasu bayanai masu muhimmanci da ke taimaka wa ci-gaban ƙasa ba.

“Duk da cewa Nijeriya tana martaba haɗin gwiwarta da Bankin Duniya kuma tana jin daɗin gudunmawar da yake bayarwa kan manufofinta, dole a sanya alƙaluman da aka ambato cikin yanayi da ya dace,” in ji Dare.

Fadar gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa adadin mutum miliyan 139 da rahoton ya ambato an samo shi ne bisa ma’aunin talauci na duniya kan $2.15 ga ko wane mutum ɗaya a yini wanda aka tsara a shekarar 2017, kuma bai kamata a yi amfani da shi wajen ƙirga adadin talakawa a Nijeriya ba.

Sunday Dare ya bayyana cewa idan aka sauya kuɗin zuwa naira kuma aka yi lissafa $2.15 zuwa kwana talatin, za ta kai $64.5, wato tana daidai da kimanin naira 100,000, kuɗin da ya zarta albashi mafi ƙanƙanta a Nijeriya naira N70,000.

“Dole a yi taka-tsan-tsan wajen fassara alƙaluman Bankin Duniya kai-tsaye,” in ji shi.

“An samo ƙiyasin ne daga ma’aunin talauci na duniya na $2.15 ga ko wane mutum, ƙiyashin da aka tsara a shekarar 2017,” in ji Dare.

Ya ƙara da cewa auna talauci bisa tsarin ƙimar kuɗi da bankin ya yi amfani da shi yana amfani ne da alƙaluman tarihin yadda ake kashe kuɗi (a shekarun 2028/19 ne Nijeriya ta tattara irin waɗannan bayanan) kuma yawanci ba ya mayar da hankali kan hada-hadar kuɗi na tsarin kan titi da na kamfanoni wanda a kansa ne miliyoyin iyalai suka dogara.

Saboda haka gwamnatin tana ganin alƙaluman sun bi ƙiyasin duniya ne, maimakon bayyana haƙiƙanin halin da ake ciki a Nijeriya a shekarar 2025 a cewar Sunday Dare.

Rumbun Labarai
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Samaila Bagudo: 'Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla