| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
Alƙalin kotun ya ce masu shigar da ƙara sun kawo shaidun da suka nuna cewa Nnamdu Kanu ya tunzura munanan hare-haren kan jami'an tsaro da kuma 'yan Nijeriya da ke kudu maso gabashin Nijeriya.
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
An kama Kanu a karon farko a 2015, amma ya tsere daga Nijeriya yayin da yake a kan beli a 2017.
20 Nuwamba 2025

Wata Babbar Kotun Tarayyar Nijeriya a ranar Alhamis ta yanke wa jagoran ‘yan-awaren Biafra Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai.

Wannan hukuncin na zuwa ne bayan shafe shekaru ana gudanar da shari’ar Mista Kanu.

Mai Shari’a James Omotosho wanda ya yanke hukuncin ya bayar da umarni kan a saka ido kan Kanu a gidan yari sannan kada a ba shi damar amfani da waya ko kuma wata na’urar sadarwa.

Alkalin ya ce ko da za a bayar da wannan damar ga Kanu sai da sahalewa da kuma sa ido na ofishin babban mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

Tun da fari gabanin yanke hukuncin, Alkalin ya ce ya samu shugaban 'yan-aware da ke fafutukar kafa ƙasar da laifukan da suka shafi ta'addanci.

Omotosho ya ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da cewa maganganun da Kanu ya yi a rediyo da umarnin da ya bayar daga ƙungiyarsa ta Indigenous People of Biafra (IPOB) wadda a yanzu aka haramta ayyukanta, sun haddasa hare-haren da suka yi sanadiyyar mutuwar jami'an tsaro da fararen-hula a yankin kudu maso gabas a cikin ƙoƙarinsa na neman kafa ƙasar Biafra mai cin gashin kanta.

Yunkurin yankin na ɓallewa a matsayin Jamhuriyar Biafra a 1967 ya haifar da yaƙin basasa na shekaru uku wanda ya kashe fiye da miliyan ɗaya.

An kama Kanu a karon farko a 2015, amma ya tsere daga Nijeriya yayin da yake a kan beli a 2017.

Daga bisani an sake kama shi a Kenya a 2021, sannan aka tuhume shi a Nijeriya da laifukan ta'addanci guda bakwai. Kanu ya musanta waɗannan tuhume-tuhumen.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?