Wata kotu a Mali ta yanke wa wani jami'i a ofishin jakadancin Faransa hukuncin zaman gidan yari na shekaru 20 kan zargin yin leƙen asiri da “zagon ƙasa ga tsaron ƙasa”.
An tsare shi tun lokacin da aka kama shi a watan Agustan 2025, kuma a ranar Alhamis an ci tarar sa da dalar Amurka 6,225 tare da hana shi shigowa Mali na tsawon shekaru 20.
A lokacin da aka kama shi, hukumomin Mali sun zargi jami'in, wanda aka bayyana da sunan shi da Yann V., da aiki ga hukumomin leƙen asirin Faransa, sannan hukumomin na Mali sun soki “ƙasashen waje” da ke ƙoƙarin kawo rashin kwanciyar hankali a ƙasar.
An tsare shi a ranar 13 ga Agusta tare da wasu jami'an Mali da ake zargin suna shirya juyin mulki a ƙasar.
Faransa ta sake jaddada cewa tuhumar da ake yi wa jami'in, wanda yake aiki a ofishin jakadancin Faransa a babban birnin Bamako, ba ta da tushe.
Ma'aikatar Harkokin Wajen Faransa a ranar Jumma’a ta ce: “Ma’aikacinmu na fuskantar shari'a kan tuhume-tuhume marasa tushe.”
“Jami'inmu yana aiwatar da aikin haɗin gwiwar tsaro kuma a kowane hali Faransa ba ta taka rawa ba — kai tsaye ko a kaikaice — wajen lalata zaman lafiyar Mali,' in ji ma'aikatar.













