| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Mali ta ɗaure jami'in diflomasiyyar Faransa shekara 20 a gidan yari kan zargin neman haddasa rikici
Mali na zargin jami'in na ƙasar Faransa da aiki tare da Hukumar Leƙen Asiri ta Faransa domin neman hargitsa ƙasar.
Mali ta ɗaure jami'in diflomasiyyar Faransa shekara 20 a gidan yari kan zargin neman haddasa rikici
Hoton birnin Bamako na kasar Mali da aka dauka daga sama. / Reuters

Wata kotu a Mali ta yanke wa wani jami'i a ofishin jakadancin Faransa hukuncin zaman gidan yari na shekaru 20 kan zargin yin leƙen asiri da “zagon ƙasa ga tsaron ƙasa”.

An tsare shi tun lokacin da aka kama shi a watan Agustan 2025, kuma a ranar Alhamis an ci tarar sa da dalar Amurka 6,225 tare da hana shi shigowa Mali na tsawon shekaru 20.

A lokacin da aka kama shi, hukumomin Mali sun zargi jami'in, wanda aka bayyana da sunan shi da Yann V., da aiki ga hukumomin leƙen asirin Faransa, sannan hukumomin na Mali sun soki “ƙasashen waje” da ke ƙoƙarin kawo rashin kwanciyar hankali a ƙasar.

An tsare shi a ranar 13 ga Agusta tare da wasu jami'an Mali da ake zargin suna shirya juyin mulki a ƙasar.

Faransa ta sake jaddada cewa tuhumar da ake yi wa jami'in, wanda yake aiki a ofishin jakadancin Faransa a babban birnin Bamako, ba ta da tushe.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Faransa a ranar Jumma’a ta ce: “Ma’aikacinmu na fuskantar shari'a kan tuhume-tuhume marasa tushe.”

“Jami'inmu yana aiwatar da aikin haɗin gwiwar tsaro kuma a kowane hali Faransa ba ta taka rawa ba — kai tsaye ko a kaikaice — wajen lalata zaman lafiyar Mali,' in ji ma'aikatar.

Rumbun Labarai
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi
Yadda abinci ke yin kisan mummuƙe a Afirka
Burkina Faso ta kawo ƙarshen dangantakar diflomasiyya da Faransa
Fiye da mutum 1,400 sun tsere daga jihar North Darfur ta Sudan a yini ɗaya yayin da ake zafafa yaƙi
Nijeriya da ƙasashe 4 sun ƙaddamar da sabuwar hukuma kan hanyar Abidjan zuwa Lagos ta $16bn
Nijar ta gabatar da takardar buƙatar ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya, ICC
An ci gaba da amfani da cin zarafin jinsi a matsayin makamin yaƙi a Sudan: MDD
Manyan Jami’o’in Afirka: Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a awon matsayi na baya bayan nan