AFIRKA
2 minti karatu
Hare-haren RSF sun kashe gomman mutane a yankin Darfur na Sudan: Likitoci
Cibiyar Likitocin Sudan (Sudan Doctors Network) ta ce cikin waɗanda suka jikkata akwai yara bakwai da mace mai juna biyu, a harin da aka kai unguwannin zama na Al Fasher, babban birnin Arewacin Darfur da ke yammacin Sudan.
Hare-haren RSF sun kashe gomman mutane a yankin Darfur na Sudan: Likitoci
Tun daga tsakiyar watan Afrilun 2023, rikici tsakanin Sojojin Sudan da dakarun RSF ya kashe mutane fiye da mutum 20,000.
6 Oktoba 2025

Aƙalla fararen hula 13 aka kashe, wasu 19 kuma suka jikkata a harin bam da dakarun Rapid Support Forces (RSF) suka kai a Arewacin Darfur, in ji likitocin yankin a ranar Litinin.

Cibiyar Likitocin Sudan (Sudan Doctors Network) ta ce cikin waɗanda suka jikkata akwai yara bakwai da mace mai juna biyu, a harin da aka kai unguwannin zama na Al Fasher, babban birnin Arewacin Darfur da ke yammacin Sudan.

Kungiyar ta ce akwai fararen hula da dama da suka maƙale a yayin da ake ci gaba da kai hari a yankin.

Ta yi Allah wadai da harin RSF a matsayin “laifin yaƙi cikakke da kuma kai tsaye a kan rayukan fararen hula, a daidai lokacin da ƙasashen duniya suka yi shiru da nuna gazawarsu wurin kare dubban mazauna da suka makale a cikin birnin.”

20,000 sun mutu, miliyan 15 sun rasa muhallansu

Kungiyar ta roƙi al’ummar duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya su ɗauki mataki nan take don dakatar da hare-hare kan fararen hula, tare da samar da kariya ta inganci ga jama’a da ma’aikatan lafiya.

RSF ta ƙaƙaba wa birnin Al Fasher takunkumi tun daga ranar 10 ga Mayun 2024, duk da gargaɗin ƙasashen duniya game da hatsarin da ke tattare da birnin, wanda ke zama cibiyar ayyukan agaji ga jihohi biyar na Darfur.

Tun daga tsakiyar watan Afrilun 2023, rikicin da ya barke tsakanin sojojin Sudan da RSF ya kashe fiye da mutane 20,000, yayin da kimanin mutane miliyan 15 suka rasa matsugunansu, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin cikin gida. Wani bincike daga jami’o’in Amurka kuma ya kiyasta adadin mutanen da suka mutu ya kai kusan 130,000.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya