| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Hare-haren RSF sun kashe gomman mutane a yankin Darfur na Sudan: Likitoci
Cibiyar Likitocin Sudan (Sudan Doctors Network) ta ce cikin waɗanda suka jikkata akwai yara bakwai da mace mai juna biyu, a harin da aka kai unguwannin zama na Al Fasher, babban birnin Arewacin Darfur da ke yammacin Sudan.
Hare-haren RSF sun kashe gomman mutane a yankin Darfur na Sudan: Likitoci
Tun daga tsakiyar watan Afrilun 2023, rikici tsakanin Sojojin Sudan da dakarun RSF ya kashe mutane fiye da mutum 20,000.
6 Oktoba 2025

Aƙalla fararen hula 13 aka kashe, wasu 19 kuma suka jikkata a harin bam da dakarun Rapid Support Forces (RSF) suka kai a Arewacin Darfur, in ji likitocin yankin a ranar Litinin.

Cibiyar Likitocin Sudan (Sudan Doctors Network) ta ce cikin waɗanda suka jikkata akwai yara bakwai da mace mai juna biyu, a harin da aka kai unguwannin zama na Al Fasher, babban birnin Arewacin Darfur da ke yammacin Sudan.

Kungiyar ta ce akwai fararen hula da dama da suka maƙale a yayin da ake ci gaba da kai hari a yankin.

Ta yi Allah wadai da harin RSF a matsayin “laifin yaƙi cikakke da kuma kai tsaye a kan rayukan fararen hula, a daidai lokacin da ƙasashen duniya suka yi shiru da nuna gazawarsu wurin kare dubban mazauna da suka makale a cikin birnin.”

20,000 sun mutu, miliyan 15 sun rasa muhallansu

Kungiyar ta roƙi al’ummar duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya su ɗauki mataki nan take don dakatar da hare-hare kan fararen hula, tare da samar da kariya ta inganci ga jama’a da ma’aikatan lafiya.

RSF ta ƙaƙaba wa birnin Al Fasher takunkumi tun daga ranar 10 ga Mayun 2024, duk da gargaɗin ƙasashen duniya game da hatsarin da ke tattare da birnin, wanda ke zama cibiyar ayyukan agaji ga jihohi biyar na Darfur.

Tun daga tsakiyar watan Afrilun 2023, rikicin da ya barke tsakanin sojojin Sudan da RSF ya kashe fiye da mutane 20,000, yayin da kimanin mutane miliyan 15 suka rasa matsugunansu, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin cikin gida. Wani bincike daga jami’o’in Amurka kuma ya kiyasta adadin mutanen da suka mutu ya kai kusan 130,000.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata