| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
An kashe sojoji 15 a harin 'yanta'adda a Jamhuriyar Benin
Ƙungiyar ‘yanta’addan mai alaƙa da Al Qaeda ta ɗauki alhaƙin kai harin da aka kai ranar Laraba a wani sansani kusa da Kofouno, da ke iyakar ƙasar da Jamhuriyar Nijar.
An kashe sojoji 15 a harin 'yanta'adda a Jamhuriyar Benin
Aƙalla sojoji 15 aka kashe a wani harin 'yan ta'adda a Benin, in ji soji ranar 5 ga watan Maris, 2026 / Reuters
6 Maris 2026

'Yanta'adda masu alaƙa da ƙungiyar Al Qaeda sun kashe sojoji 15 a wani hari da suka kai a wani sansanin soji a arewacin Jamhuriyar Benin, kamar yadda rundunar sojin ƙasar ta bayyana ranar Alhamis.

Ƙungiyar ‘yanta’addan mai alaƙa da Al Qaeda ta ɗauki alhaƙin kai harin da aka kai ranar Laraba a wani sansani kusa da Kofouno, da ke iyakar ƙasar da Jamhuriyar Nijar.

Mai magana da yawun soji, Kanal James Johnson ya shaida wa kamfanin dillancin labaran AFP ranar Laraba cewa harin ya jikkata sojoji biyar, “amma ba sa fuskantar barazanar mutuwa."

Wata majiyar soji wadda aka tura yankin ta shaida wa kamfanin dillancin labaran AFP cewa harin ya laƙume rayuka da yawa, inda take magana bisa sharaɗin sakaye sunanta.

"A halin yanzu muna kan share yankin," in ji majiyar.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab
Mali ta musanta rahoton sakin ’yanta’adda 200 domin samun man fetur
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Darasin da Togo ke koya wa sauran kasashe wajen magance cututtukan da aka yi watsi da su
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka