| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
NCC ta gargaɗi masu gini da aikin hanya kan lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa a Nijeriya
A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, NCC da NSCDC sun bayyana layukan sadarwan na ƙarƙashin ƙasa a matsayin muhimman kadarorin ƙasa, waɗanda ke tallafa wa tattalin arzikin fasahar zamani na Nijeriya da harkokin kasuwanci.
NCC ta gargaɗi masu gini da aikin hanya kan lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa a Nijeriya
Hukumomin sun bayyana cewa ba za a lamunci ci gaba da lalata layukan sadarwan ba / Others
5 Fabrairu 2026

Hukumar Kula da Sadarwa ta Nijeriya (NCC) da Hukumar Kare Farar-Hula ta Nijeriya (NSCDC) sun gargadi kamfanonin gine-gine da sauran masu ayyukan injiniya da su guji lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa na fibre-optic yayin aikin gyaran hanyoyi da sauran ayyukan gine-gine, inda suka ce masu aikata hakan na iya fuskantar hukunci a kotu.

Hukumomin sun bayyana cewa ba za a lamunci ci gaba da lalata layukan sadarwan ba, wanda galibi ana yi ne saboda da sakaci inda suka jaddada cewa lalata layukan laifi ne.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, NCC da NSCDC sun bayyana layukan sadarwan na ƙarƙashin ƙasa a matsayin muhimman kadarorin ƙasa, waɗanda ke tallafa wa tattalin arzikin fasahar zamani na Nijeriya da harkokin kasuwanci da kuma kuma taimaka wa sadarwar gwamnati.

Sun yi gargaɗin cewa lalata waɗannan kayayyakin more rayuwar na iya jefa tsaron ƙasa zaman da tattalin arziki da lafiyar jama’a cikin hadari.

Hukumomin sun ƙara da cewa, karkashin dokar kare kayayyakin sadarwa masu muhimmanci na ƙasa ta (CNII) Order 2024, an ayyana layukan sadarwar na fibre-optic a matsayin muhimman kayayyakin sadarwa na ƙasar.

Saboda haka, idan an lalata su sakamakon haƙar ƙasa ko ayyukan gini ko kuma rashin tutuɓar hukumomin da abin ya shafa, hakan zai iya zama aikata laifi.

Sun ƙara da cewa duk wanda aka samu da laifi — ko mutum ɗaya, kamfanin gine-gine ko dan kwangilar gwamnati — zai fuskanci hukunci da sauran matakan doka kamar yadda dokoki suka tanada..

 

 

Rumbun Labarai
Jami’an tsaron Nijeriya sun kwance wani bam da ‘yan ta’adda suka dasa a Zamfara
Nijeriya ta ƙaddamar da tsarin tattalin arzikin halal domin bunƙasa arzikin ƙasar
Solar Halo: Yadda mazauna birnin Jos a Nijeriya suka ga al'ajabin rabuwar Rana gida uku
Kotu ta umarci Birtaniya ta biya diyyar £420m ga iyalan masu haƙar kwal 21 a Nijeriya
Jamhuriyar Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta'addanci da ya kashe mutum 170 a Nijeriya
NNPC na tattaunawa da kamfanin China domin farfaɗo da matatun man Nijeriya
Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji Jihar Kwara
Mummunan harin ta'addanci ya kashe fiye da mutum 160 a Jihar Kwara ta Nijeriya
Annobar cizon maciji a Nijeriya: Abin da ya sa mutuwar mawaƙiya Nwangene ta zama kiran ɗaukar mataki
Rundunar sojin Amurka tabbatar da tura 'wata ƙaramar tawaga' Nijeriya
'Yan fashin daji sun kashe mutum 30 a hare-haren da suka kai a Katsina da Kwara
Kotun Nijeriya ta tuhumi tsohon ministan shari'a Malami da laifukan ta'addanci
An gurfanar da mutum 9 a kotu bisa zargin kisan mutum 150 a Yelwata na jihar Benue a 2025
Gomman masu ibada da ake fargaba an yi garkuwa da su daga cocin Kurmin Wali sun koma gida
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan Boko Haram, Abu Khalid a Sambisa
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan ISWAP a arewa maso gabas
Daga tsaro zuwa kasuwanci: Abin da ya sa juyawar Nijeriya zuwa Turkiyya ke da muhimmanci
Nijeriya da Saudiyya sun sanya hannu kan yarjejeniyar ɗaukar ma'aikata a karon farko
Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za ta warware rikicin Masarauta
‘Yansandan Nijeriya sun ƙwato kwamfuta 400, sun kama ɓarayin airtime na Naira biliyan 7.7