| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Cocin Katolika reshen Kafanchan ta ce mutum goma ne aka sace, amma ‘yansanda sun ce biyar ne, sannan mutanen da aka kashe biyu sojoji ne ɗaya kuma ɗansanda.
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Wani mai magana da yawun 'yansandan Kaduna ya tabbatar da lamarin / Reuters
8 awanni baya

‘Yanbindiga sun kashe mutane uku kuma sun sace wani faston Katolika da wasu mutane yayin wani harin da suka kai a da sanyin safiya a gidan faston a jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, in ji majiyoyin coci da 'yan sanda a ranar Lahadi.

Harin wanda aka kai a ranar Asabar a Ƙaramar Hukumar Kauru ya nuna yadda rashin tsaro ke ƙara ƙaruwa a yankin, kuma ya zo 'yan kwanaki bayan jami'an tsaro sun kuɓutar da duka masu ibada 166 da aka sace a hare-haren da ‘yanbindiga suka kai kan wasu coci biyu a wasu sassa na Kaduna.

Harin asubahi

Cocin Katolika reshen Kafanchan ta bayyana cewa limamin da aka sace shi ne Nathaniel Asuwaye, wanda fasto ne a cocin Holy Trinity Catholic Church a Karku, kuma ta ce wasu mutane 10 an sace su.

An kashe mazauna uku yayin harin, wanda ya fara kusan karfe 3:20 na safe (0220 GMT), in ji sanarwar cocin.

Wani mai magana da yawun 'yansandan Kaduna ya tabbatar da lamarin, amma ya ce mutum biyar ne aka sace gaba ɗaya kuma mutane ukun da aka kashe jami’an tsaro ne,

"Jami'an tsaro sun yi musayar wuta da 'yanbindiga, sun kashe wasu daga cikinsu, kuma abin takaici sojoji biyu da ɗansanda sun rasu," in ji shi.

Sakon hadin kai daga Fafaroma

Fafaroma Leo, a lokacin jawabin mako-makonsa ga mabiya a Filin St. Peter, ya nuna goyon bayansa kan waɗanda ɓarayi ke kai wa hari a Nijeriya.

"Ina fatan hukumomin da suka dace za su ci gaba da aiki da zuciya don tabbatar da tsaro da kare rayuwar kowanne ɗan ƙasa," in ji Leo.

Rumbun Labarai
Nijeriya ta ƙaddamar da tsarin tattalin arzikin halal domin bunƙasa arzikin ƙasar
Solar Halo: Yadda mazauna birnin Jos a Nijeriya suka ga al'ajabin rabuwar Rana gida uku
Kotu ta umarci Birtaniya ta biya diyyar £420m ga iyalan masu haƙar kwal 21 a Nijeriya
NCC ta gargaɗi masu gini da aikin hanya kan lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa a Nijeriya
Jamhuriyar Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta'addanci da ya kashe mutum 170 a Nijeriya
NNPC na tattaunawa da kamfanin China domin farfaɗo da matatun man Nijeriya
Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji Jihar Kwara
Mummunan harin ta'addanci ya kashe fiye da mutum 160 a Jihar Kwara ta Nijeriya
Annobar cizon maciji a Nijeriya: Abin da ya sa mutuwar mawaƙiya Nwangene ta zama kiran ɗaukar mataki
Rundunar sojin Amurka tabbatar da tura 'wata ƙaramar tawaga' Nijeriya
'Yan fashin daji sun kashe mutum 30 a hare-haren da suka kai a Katsina da Kwara
Kotun Nijeriya ta tuhumi tsohon ministan shari'a Malami da laifukan ta'addanci
An gurfanar da mutum 9 a kotu bisa zargin kisan mutum 150 a Yelwata na jihar Benue a 2025
Gomman masu ibada da ake fargaba an yi garkuwa da su daga cocin Kurmin Wali sun koma gida
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan Boko Haram, Abu Khalid a Sambisa
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan ISWAP a arewa maso gabas
Daga tsaro zuwa kasuwanci: Abin da ya sa juyawar Nijeriya zuwa Turkiyya ke da muhimmanci
Nijeriya da Saudiyya sun sanya hannu kan yarjejeniyar ɗaukar ma'aikata a karon farko
Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za ta warware rikicin Masarauta
‘Yansandan Nijeriya sun ƙwato kwamfuta 400, sun kama ɓarayin airtime na Naira biliyan 7.7