| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Shugaban Iran ya yi alƙawarin ba za su yi saranda ba, ya ba ƙasashe maƙwabta haƙuri
Iran ta ce ba za ta sake kai hari kan ƙasashe makwabta ba kuma ba za ta harba makami mai linzami a kansu ba sai dai idan harin da aka kai kan Iran ya fito daga ƙasashen na Gulf, in ji Shugaban Iran Masoud Pezeshkian.
Shugaban Iran ya yi alƙawarin ba za su yi saranda ba, ya ba ƙasashe maƙwabta haƙuri
Pezeshkian yana ɗaya daga cikin mutane uku na wata majalisa ta riƙon kwarya da ke shugabantar Iran bayan an kashe Khamenei. / AP
11 awanni baya

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian a ranar Asabar ya bayyana cewa ƙasar tasa ba za ta taɓa mika wuya ga Isra'ila da Amurka ba, yayin da yaƙin ya shiga mako na biyu.

Ya bayyana cewa, "dole ne ƙawayen Iran su tafi ƙabari da burinsu na ganin mutanen Iran sun miƙa wuya ba tare da sharadi," kamar yadda Pezeshkian ya bayyana, a cikin jawabin da aka watsa a gidan talabijin na ƙasar.

Isra'ila da Amurka sun kai farmaki kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu inda suka kashe Jagoran Addini na Iran, Ali Khamenei inda hakan ya haddasa rikici a yankin.

Tun daga lokacin, Iran ta mayar da martani da harin makami masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa a kan Isra'ila da wuraren Amurka a ƙasashen yankin na Gulf.

Pezeshkian na daga cikin mambobi uku na kwamitin shugabanci na wucin-gadi da ke jagorantar Iran tun bayan kisan Khamenei.

A lokacin jawabin, Pezeshkian ya nemi afuwa daga ƙasashen makwabta saboda hare-haren da Iran ta kai a faɗin yankin, yana mai cewa ba za a ci gaba da kai musu hare-hare ba sai dai idan hare-haren sun fito daga gare su.

"Dole ne na nemi afuwa a madadina da kuma a madadin Iran ga ƙasashen maƙwabta waɗanda Iran ta kai musu hari," in ji shi.

"Kwamitin shugabancin wucin-gadi ya yanke hukunci a jiya cewa ba za a sake kai hari kan ƙasashe makwabta ba kuma ba za a harba makami mai linzami ba sai dai idan harin da aka kai kan Iran ya fito daga wadancan ƙasashen," in ji shi.

Rumbun Labarai
Ankara na da ‘yancin mayar da martani don kare Turkiyya daga yaƙin Amurka-Isra'ila da Iran
Iran ta ce ta kai wa jirgin ruwan dakon mai na Amurka hari a Gulf
Mafi yawan Amurkawa ba sa goyon bayan yaƙin Amurka kan Iran: Ƙuri'ar jin ra'ayi
Iran ta yi iƙirarin kashe sojojin Amurka 500 a cikin kwanaki biyar na yaƙi
Shin yaƙin Amurka da Isra’ila a Iran duk dabara ce ta sake mamayar yankin Gabas ta Tsakiya?
'An gaya wa dakarun Amurka cewa yaƙin Iran ‘ƙudirar Ubangiji’ ce don kawo ƙarshen duniya'
Amurka ta yi asarar kayayyakin sojin na kusan $2bn a kwanaki 4 na yaƙi da Iran
Iran ta ce babu zancen tattaunawa da Amurka, ta sha alwashin kare kanta kawai
Ministan Turkiyya Fidan na yin tuntubar diflomasiyya a tsaka da hare-haren Amurka da Isra’ila a Iran
Yaƙin Iran da Isra'ila ya sa tafiya Umara zuwa Saudiyya na fuskantar barazana
Iran ta ce ta kai hari a wurare aƙalla 500 na Isra'ila da Amurka
Ƙasashen Afirka sun yunƙura don kare jama'arsu da ke  Gabas ta Tsakiya
Me ya rage wa Iran bayan Khamenei?
Jiragen yaƙin Amurka da dama sun faɗi a Kuwait, in ji ma'aikatar tsaron Kuwait
Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar
Iran ta kafa majalisar jagorancin wucin-gadi a Iran bayan kashe Khamenei
Nijeriya, Senegal da Libya sun buƙaci a tsagaita wuta yayin da Isra'ila-Amurka ke rikici da Iran
Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra'ila sun kashe Khamenei
Iran ta tabbatar da kisan Ali Khamenei da iyalansa
Iran ta musanta iƙirarin Amurka da Isra'ila na kashe Jagoran Addini Ali Khamenei