NIJERIYA
2 minti karatu
An kashe mutum 17 a yankin Birnin Gwari na Jihar Kaduna sakamakon arangama da ‘yan bindiga
Tashin hankalin ya fara ne a lokacin da wani gawurtaccen shugaban ɓarayin daji ya yi ƙoƙarin ƙwatar zinari daga hannun masu haƙar ma’adinai ta hanyar yi musu barazana da bindiga.
An kashe mutum 17 a yankin Birnin Gwari na Jihar Kaduna sakamakon arangama da ‘yan bindiga
Yankin Birnin Gwari ya sharara wurin rashin tsaro musamman garkuwa da mutane
18 Oktoba 2025

Aƙalla mutum 17 sun rasa rayukansu a wata mummunar arangama da ta faru tsakanin ’yan ta’adda da masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a wani wurin da ake haƙar zinari a Jihar Kaduna, bisa wani rahoton tsaro na sirri da aka shirya wa Majalisar Ɗinkin Duniya a ranar Juma’a.

Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis a Birnin Gwari, wani yanki a arewa maso yammacin Nijeriya da ya daɗe yana fama da ta’addanci, satar shanu, da kuma sace mutane domin neman kuɗin fansa.

A cewar kafar watsa labarai ta TVC News ta Nijeriya, tashin hankalin ya fara ne a lokacin da wani gawurtaccen shugaban ɓarayin daji ya yi ƙoƙarin ƙwatar zinari daga hannun masu haƙar ma’adinai ta hanyar yi musu barazana da bindiga.

Sai dai masu haƙar ma’adinan sun ƙi yarda inda suka far masa har suka kashe shi. Wannan kisan ya tayar da hankali, inda ’yan tawagar shugaban da aka kashe suka dawo da makamai, suka kai farmaki suka kashe masu haƙar ma’adinai bakwai.

Washe gari rikicin ya bazu zuwa kauyen Layin Danauta da ke kusa. Maharan sun kashe mutane tara sannan suka jikkata mutum 13, sannan suka sace wasu mazauna garin, tare da lalata gidaje da dukiyoyi. 

Yankin Birnin Gwari, wanda ke da albarkatun ƙasa da ƙasar noma, ya dan samu zaman lafiya bayan gwamnatin Jihar Kaduna ta sanya hannu a yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindiga da al’ummomin yankin a Nuwamba 2024.

Sai dai wannan sabon tashin hankali ya tayar da hankalin jama’a, inda wani mazaunin yankin mai suna Muhammad Kabir, ya bayyana damuwarsa kan wannan tashin hankali.

 “Mun samu dan zaman lafiya tun bayan yarjejeniyar sulhu, amma wannan sabon tashin hankali yana iya kawo cikas ga zaman lafiyar,” in ji Kabir.

Abin da ke ƙara rikitar da lamarin yankin shi ne kasancewar ’yan ta’addar Ansaru, wata ƙungiya da ke da alaƙa da Al-Qaeda. Tun daga shekara ta 2021, rahotanni sun nuna cewa Ansaru ta kulla dangantaka da wasu kungiyoyin ’yan bindiga a yankin.

Ko da yake yawancin ’yan bindiga suna aiki ne saboda ribar kuɗi, ba saboda akida ba, masana tsaro sun gargaɗi cewa ƙarfafa alaƙa tsakanin su da kungiyoyin ta’addanci daga arewa maso gabas na iya ƙara tabarbarewar tsaro a yankin.

Rumbun Labarai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Samaila Bagudo: 'Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla
‘Yan sandan Nijeriya sun ceto ‘yan kasashen waje 23 da aka yi garkuwa da su