| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka ya yi Allah wadai da boren da aka yi a Nijar
Boren ya yi sanadin mutuwar mutane biyar, a cewar rahotannin kafofin watsa labarai.
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka ya yi Allah wadai da boren da aka yi a Nijar
Kungiyar AU ta jaddada kiranta na "dawo da tsarin mulki" a Nijar.

Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ya bayyana damuwarsa bayan wani boren da aka daƙile shi a Nijar, yana mai Allah wadai da duk wani yunƙuri na kwace mulki da ƙarfi.

A ranar Asabar, ma’aikatar tsaron ƙasar ta ce dakarun gwamnati sun yi nasarar daƙile boren da wasu sojoji a cikin rundunoninsu suka yi.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, ƙungiyar AU ta ce shugabanta, Mahmoud Ali Youssouf, yana bibiyar tashe-tashen hankulan da suka faru a wurare masu mahimmanci a babban birnin Nijar, Yamai, "cikin damuwa".

Masu AlakaTRT Afrika - Boren soji a Yamai: AES ta jaddada goyon bayanta ga Nijar, ta yaba wa martanin dakarun tsaro

"Shugaban... ya yi Allah wadai da amfani da tashin hankali da duk wani yunƙuri na kwace mulki da ƙarfi. Yana mai kira ga dukkan masu hannu a cikin lamarin da su yi taka tsantsan tare da kare tsaro da kwanciyar hankalin al’umma a ƙasar," in ji sanarwar.

'Tsarin kundin tsarin mulki'

Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyar, a cewar rahotannin kafofin watsa labarai.

An kashe dakarun fadan shugaban ƙasa uku a boren, a cewar kamfanin dillancin labarai na ƙasar ANP.

Kazalika AU ta kuma jaddada kiranta na "maido da tsarin mulki".

Kawo yanzu dai Janar Abdourahamane Tiani, wanda ke jagorantar gwamnatin mulkin soji a Nijar, bai fito fili ya yi magana ba tun bayan faruwar lamarin.

Sai dai ofishinsa ya ce ya yi magana ta wayar tarho a ranar Litinin da Shugaban Aljeriya Abdelmadjid Tebboune kuma ya tabbatar da cewa an tura jiragen yaƙin Aljeriya zuwa Yamai a ranar Lahadi bisa buƙatar Nijar.

Masu AlakaTRT Afrika - Algeria ta aika jiragen yaƙi huɗu zuwa Jamhuriyar Niger bayan tashin hankali a Niamey

Ma'aikatar Tsaron Aljeriya ta ce Babban Hafsan Sojojin ƙasar Said Chengriha ne ya ba da umarnin tura jiragen bisa umarnin Shugaba Abdelmadjid Tebboune don ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Aljeriya da Nijar, "musamman a fagen ayyukan tsaro na soja."