| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
Wani rahoto da ofishin kare haƙƙin bil’adama na MDD ya fitar, ya ce harin da dakarun RSF ɗin suka kai don karbe birnin Al Fasher ya ƙunshi mummunan abubuwa na zalunci wanɗanda suka haɗa da kisan kiyashi da fyade da sace mutane don neman kuɗin fansa.
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
Yan uwa suna duba sunaye a kan jakunkunan gawawwakin wadanda suka mutu a Khartoum da ke Sudan ranar 11 ga Janairun 2026. / AP
10 awanni baya

Fiye da mutane 6,000 ne suka rasa rayukansu cikin fiye da kwanaki uku lokacin da rundunar sa-kai ta RSF ta ƙaddamar da "jerin hare-hare masu tsanani" a yankin Darfur na Sudan a karshen watan Oktoba, in ji Majalisar Dinkin Duniya.

Wani rahoto da ofishin kare haƙƙin bil’adama na MDD ya fitar, ya ce harin da dakarun RSF ɗin suka kai don karbe birnin Al Fasher ya ƙunshi mummunan abubuwa na zalunci wanɗanda suke daidai da laifukan yaƙi.

“Take-hakkokin da aka yi ba tare da tausayi ba da RSF da dakarun haɗin gwiwarsu suka aikata a harin ƙarshe kan el-Fasher sun nuna cewa rashin hukunci mai ɗorewa na ƙara janyo ci gaba da samun tashin hankali,” in ji Babban Kwamishinan MDD na hukumar kare haƙƙin ɗan’adam, Volker Türk.

RSF da dakarun haɗin gwiwarsu, wanda ake kira Janjaweed, sun mamaye Al Fasher, abin da ya rage wa sojojin Sudan a Darfur, a ranar 26 ga Oktoba kuma suka yi barna a cikin birnin da kewayensa bayan shafe fiye da watanni 18 suna yi masa ƙawanya.

Rahoton MDD mai shafi 29 ya bayyana jerin mummunan al'amura waɗanda suka haɗa da kisan kiyashi da fyade da sace mutane don neman kuɗin fansa da azabtarwa da rashin tausayi zuwa tsarewa da ɓacewar mutane. A lokuta da dama, harin ya kasance na kabilanci, in ji rahoton.

Rumbun Labarai
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar
Sudan ta sake buɗe filin jiragen sama na Khartoum bayan yaƙin kusan shekaru uku
Nijar: Ƙungiyar Daesh ta ɗauki nauyin harin da aka kai sansanin sojin sama na Yamai
Fiye da mutum 200 sun rasu bayan ruftawar wurin haƙar coltan a Jamhuriyar Kongo
Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta sha alwashin goyon bayan Nijar bayan kai hari a filin jirgin saman Yamai
Nijar ta zargi Faransa, Benin da Côte d'Ivoire da taimaka wa maharan filin jiragen sama