Ƙungiyar RSF ta kai mummunan hari wani ƙauye a Darfur ta Arewa

'Yan-awaren ƙungiyar RSF sun kai hari ƙauyen Mastariha suka kuma ƙona gidaje da yawa, in ji wata kungiya mai zaman kanta ta Emergency Lawyers.

By
Ƙungiyar RSF ta kai mummunan hari wani ƙauye a Darfur ta Arewa / Reuters

Wata ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta Sudan a ranar Talata ta zargi ƙungiyar ‘yan-awaren Rapid Support Forces (RSF), da kai wani mummunan hari ƙauyen Mastariha a Arewacin Darfur, a yammacin Sudan.

Kungiyar Emergency Lawyers (Lauyoyi na Gaggawa), wata ƙungiya mai zaman kanta, ta ce a cikin wata sanarwa cewa mayaƙan RSF sun kai farmaki Mastariha a ranar Litinin sannan suka ƙona gidaje da dama a ƙauyen.

Sanarwar ta ƙara da cewa kafin farmakin an fara da harin jiragen sama marasa matuki a wurare da dama, ciki har da cibiyar lafiya, kasuwa, wuraren masaukin baƙi da gidajen mutane, wanda hakan ya jawo raunuka da mutuwar wasu tare da tilasta wa da dama tserewa.

Ƙungiyar ta kira harin a matsayin "keta dokokin jinƙai na ƙasa da ƙasa da take haƙƙin ɗan’adam a fili."

Kira don bincike

“Wannan hari ya ƙara shiga tarihin keta dokoki a Darfur, wanda zai iya zama kisan kare dangi da laifukan da suka kai matsayin laifukan ƙasa da ɗan’adam, kuma yana nuna tsarin kai hare-hare ga fararen hula da dukiyoyinsu,” in ji ƙungiyar, tana kiran Kotun Duniya ta Hukunta Manyan Laifuka (ICC) da ta gudanar da bincike kan laifukan da aka aikata a Darfur, kuma ta gurfanar da waɗanda ke da alhaki kai-tsaye don tabbatar da kariyar fararen-hula.

Wasu 'yan RSF da dama sun kuma saka bidiyo daga Mastariha, in ji Hukumar Labarai ta Anadolu.

Sojoji suna riƙe da iko a mafi yawan jihohin Sudan, ciki har da babban birni Khartoum, yayin da RSF ke riƙe da jihohi biyar na Darfur ta yamma, sai dai wasu sassan Arewacin Darfur da suka kasance ƙarƙashin ikon rundunar soja.

Rikicin Sudan, wanda aka fara a watan Afrilun 2023, ya kashe dubban mutane kuma ya tilasta wa kusan mutane miliyan 13 yin gudun hijira, inda ya haifar da ɗaya daga cikin mafi munin rikicin jinƙai a duniya da yanayin yunwa, a cewar rahotannin Majalisar Dinkin Duniya.