| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
An jikkata sojojin Isra’ila takwas yayin kutse a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Sojojin Isra'ila na ci gaba da kai hare-hare kowace rana a Lebanon tare da rushe gidaje suna karya yarjeeniyar tsagaita wuta ta 17 ga Afrilu.
An jikkata sojojin Isra’ila takwas yayin kutse a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Motar sojojin Isra'ila ke ruguje gine-gine a kudancin Lebanon a ranar 30 ga Afrilun 2016. / Reuters

Akalla sojojin Isra'ila takwas ne suka ji rauni a fafatawar da suka yi da mayakan Hezbollah a arewacin kogin Litani da ke kudancin Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta na ɗan lokaci, a cewar kafofin watsa labarai na Isra'ila.

Gidan rediyon sojoji da Channel 14 a ranar Talata sun bayyana cewa sojojin sun ji rauni a wasu fafatawa uku kai tsaye da Hezbollah.

Rikicin ya barke ne bayan da sojoji daga rundunar Golani da rundunar Egoz suka ketare kogin Litani zuwa wajen Zawtar al-Sharqiyah, wani ƙauye mai nisan kilomita 10 daga kan iyakar Isra'ila, a cikin abin da rediyon sojoji ta bayyana a matsayin "farmakan" "kawar da makaman roka."

An ɗauki tsawon mako guda ana kai "farmakan" kuma an raunata sojoji da dama, in ji Rediyon Sojojin.

Channel 14 ta ce sojojin Isra'ila takwas sun ji rauni a fafatawar da suka yi da mayakan Hezbollah a yankin.

Kafofin watsa labaran ba su fayyace lokacin da sojojin suka ji rauni ko kuma lokacin da aka kai wadannan farmakai ba, suna cewa an ɓoye bayanan tare da hana su buga su har zuwa ranar Talata.

Babu wani bayani nan take daga Hezbullah game da rahoton.

Tun daga ranar 2 ga Maris, hare-haren Isra'ila a Lebanon sun kashe sama da mutane 2,869, sun kuma raunata sama da mutane 8,730, sannan sun raba sama da miliyan 1.6 da gidajensu, kimanin kashi ɗaya bisa biyar na al'ummar ƙasar, a cewar bayanan mahukuntan Lebanon.

Duk da tsagaita wutar da aka sanar a ranar 17 ga Afrilu kuma aka tsawaita har zuwa ranar 17 ga Mayu, sojojin Isra'ila suna ci gaba da kai hare-hare kowace rana a Lebanon, suna faɗaɗa mamayarsu da kuma rusa gidaje a ƙauyuka da dama a kudancin Lebanon.

Rumbun Labarai
Iran ta mayar da martani ga masu shiga tsakani na Pakistan kan shawarar Amurka ta kawo ƙarshen yaƙi
Saudiyya ta musanta zargin bayar da izinin amfani da sararin samaniyarta don ayyukan soja
Iran ta harba makamai masu linzami ga sojin Amurka bayan hari kan tankar dakon manta
Darussa daga sabon tsarin tafiyar da duniya: Ba za a iya sayen tsaro ba, amma dole a gina shi
Trump ya dakatar da shirinsa na taimaka wa jiragen ruwa wucewa ta Mashigar Hormuz
Shugabannin duniya na matsa wa Iran lamba yayin da ake fargabar batun tsagaita wuta zai iya rushewa
Harin da Amurka ta kai Mashigar Hormuz ya kashe fararen-hula 5, a cewar Iran
Iran ta ce duk wani shirin Amurka kan mashigar Hormuz zai zama keta yarjejeniyar tsagaita wuta
Iran ta ba Amurka wata guda don janye toshe tashoshin ruwanta da kawo ƙarshen yaƙin Iran da Lebanon
Buɗaɗɗiyar maƙabartar Gaza: Gawawwaki 8,000 sun maƙale, yayin da aikin kwashe ɓaraguzai ya tsaya cak
Iran ta kunna na'urar tsaron sama yayin da Trump ke fuskantar wa'adin ikon shiga yaki daga Majalisa
Isra'ila na rasa goyon bayanta a tsakanin matasa 'yan  Amurka - Rahoto
Za a ci gaba da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran ta waya – Trump
Trump ya ce bai kamata Iran ta samu makamin nukiliya ba a liyafar da aka shirya wa Sarki Charles III
Netanyahu ya bayyana a kotu don shari'ar cin hanci da rashawa a karon farko tun soma yaƙin Iran
Rikicin Gabas ta Tsakiya na koyar da darasi: Turkiyya ta zama kan gaba a zaɓin ƙasashen Afirka
Trump bai yarda da tayin Iran na sake buɗe Mashigar ruwan  Hormuz ba, in ji rahotanni
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya