'Yan Somaliya sun gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
An ƙaddamar da wannan shiri ne a watan Yunin 2022, inda talakawa, waɗanda ke zaune a Somaliya da kuma waɗanda ke zaune a ƙasashen waje, suka tara kusan dala 300,000.
A wani abin da ba kasafai ake gani a duniya ba, 'yan Somali sun gina waa tsohon shugabansu Mohamed Abdullahi Mohamed, wanda aka fi sani da Farmaajo sabon gida.
Ginin wannan gidan da ‘yan ƙasar suka yi a birnin Marka mai tarihi da ke bakin Tekun Indiya, an yi shi ne gaba ɗaya ta hanyar tara gudunmawa daga jama'a.
An kaddamar da wannan yunƙuri a watan Yuni 2022, inda mutane da yawa, waɗanda ke zaune a Somalia da kuma mazauna ƙasashen waje (diaspora), suka tara kimanin dala 300,000.
An soma ginin, wanda aka sanya masa suna 'Na gode, Shugaban Ƙasa', a watan Yulin 2023, kuma an kashe kusan dala 295,000, a cewar ofishin hulɗa da jama'a na tsohon shugaban.
Sabon gidan, wanda aka gina a fili mai fadin mita 120 da tsawon mita 140 kusa da bakin teku, an buɗe shi a hukumance ranar 6 ga Fabrairu.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, tsohon shugaban ya nuna godiyarsa ta gaskiya ga dukkan 'yan Somali, fararen hula da ma mambobin jami'an tsaro, waɗanda suka ba da gudunmawa.
Farmaajo ya yi wa Somalia aiki a matsayin shugaban ƙasa na tara daga Fabrairun 2017 zuwa Mayun 2022, kuma a baya shi ne firaministan ƙasa daga 2010 zuwa 2011.
Mutanen da suka ba da gudunmawa bisa raɗin kansu don ginin sun yi amfani da damar wajen yaba wa salon shugabancinsa, suna mai cewa ya sarrafa albarkatu cikin hikima, ya inganta sunan Somalia a ƙasashen waje, kuma ya taimaka wajen rage wasu bashin ƙasashen waje.
Shugaban ƙasa na yanzu, Hassan Sheikh Mohamud, ya gaji Farmaajo, kuma tun daga lokacin yana ci gaba da ƙoƙarin farfado da Somalia daga barnar shekaru na rikice-rikice da bala'o'in ƙasa, tare da goyon bayan abokan haɗin gwiwa na ƙasa da ƙasa, ciki har da Turkiyya.
Ba kamar a yawancin ƙasashe ba, a Somalia tsoffin shugabanni ba sa samun kuɗaɗen fansho mai yawa ko kuɗaɗen tallafi bayan barin mulki.
Farmaajo ya taba bayyanawa a fili cewa bai mallaki gida a babban birnin Mogadishu ba, inda yake zaune a gidan haya tun bayan ya bar ofis.
Birnin Marka, inda aka gina sabon gidan tsohon shugaban, wurin yawon bude ido ne kuma cibiyar siyasa, domin a nan ne gidan shugaban ƙasar na farko, Aden Abdulle Hassan yake.
Masana suna cewa wannan abin da 'yan Somali suka yi wani muhimmin saƙo ne na shugabanci wanda ka iya yin tasiri ba kawai a Somalia ba har ma a Afirka gaba ɗaya.