| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
Ranar Alhamis ne dai majalisar dokokin ƙasar ta amince da sunan alƙalin da shugaban ƙasar ya miƙa mata a matsayin sabon alƙalin alƙalan ƙasar.
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
Shugaba John Mahama ya rantsar da maishari'a Baffoe-Bonnie a matsayin alƙalin alƙalan Ghana
18 Nuwamba 2025

Maishari’a Paul Baffoe-Bonnie ya kama aiki a matsayin sabon Alƙalin Alƙalan ƙasar Ghana na tara tun bayan da ƙasar ta fara jamhuriya ta huɗu.

Shugaba John Dramani Mahama ne ya rantsar da shi a fadar gwamnatin ƙasar da ke Accra  ranar Lititin a wani bikin da alƙalan manyan kotuna suka halarta tare da ‘yan’uwan alƙalin da ‘yan majalisar dokoki da manyan jami’an gwamnati.

A ranar Alhamis ne majalisar dokokin ƙasar ta amince da sunan alƙalin da Shugaban Ƙasar ya miƙa mata a matsayin sabon Alƙalin Alƙalan ƙasar.

Kafin a rantsar da shi, alƙalin yana aiki ne a matsayin muƙaddashin Alƙalin Alƙalan ƙasar tun ranar 22 ga watan Afrilun shekarar, 2025.

Da yake rantsar da Maishari’a Baffoe-Bonnie, Shugaba Mahama ya ce dole ya kasance mai ɗabi’u na adalci da ‘yanci da gaskiya kamar yadda aka tsara a kundin tsarin mulkin shekarar 1992.

Ƙarfin Dimokraɗiyyar Ghana, a cewar Shugaban Ƙasar, ya dogara ne ga ga daidaiton iko tsakanin ɓangarorin gwamnati uku – ɓangaren zartarwa da ɓangaren dokoki da kuma ɓangaren shari’a – inda za su yi aiki da ‘yanci amma kuma da haɗin kai domin jin daɗin ‘yan Ghana.

“A matsayin shugaba, na yi sha alwashin jajircewa na ga tabbatar da ‘yancin ɓangaren shari’a,” kamar yadda Shugaba Mahama ya bayyana.

“Ɓangaren shari’a mai ‘yanci ba tallafi ba ne kawai ga kotuna. Buƙata ce wadda kundin tsarin mulki ya yarda da ita da kuma kare kowane ɗan ƙasa da ciki har da Shugaban Ƙasar,” in ji shi.

Ya yi kira ga Maishari’a Baffoe-Bonnie ya aiwatar da aikinsa ba tare da sani ko sabo ba.

Yayin da mutane ke rage yarda da hukumomin gwamnati, Shugaba Mahama ya ce dole ɓangaren shari’a ya kasance ya fi ƙarfin zargi domin wani jami’in shari’a ya aikata cin hanci ɗaya zai iya lalata shekaru na aiki tuƙuru da da kuma yardar da al’umma ke da shi kan ɓangaren gabaɗaya.

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi