Matsalar yunwa a Sudan: Miliyoyin mutane na cin abinci sau ɗaya a rana
Yayin da barazanar yunwa sakamakon yaƙi ke ci gaba da ƙaruwa, ƙungiyoyin agaji na gargaɗi game da dabarun janyowa mutane yunwa da gangan, rugujewar tsarin samar da abinci, da kuma ƙaruwar matsalar rashin abinci mai gina jiki a yankunan da ake rikici.
Miliyoyin mutane a ƙasar Sudan suna rayuwa ne a kan abinci sau ɗaya kacal a rana, yayin da matsalar ƙarancin abinci da ke ƙara ta’azzara ke gab da jefa ƙasar cikin matsananciyar yunwa, a cewar wani sabon rahoto da manyan ƙungiyoyin agaji suka fitar.
Yaƙin da ake yi tsakanin sojojin Sudan da dakarun sa-kai na Rapid Support Forces (RSF), wanda yanzu haka yake shiga shekara ta uku, ya ruguza fannin noma, ya raba miliyoyin mutane da muhallansu, sannan ya haifar da ɗaya daga cikin manyan matsalolin jin ƙai mafi muni a duniya.
Rahoton ya gano cewa a yankunan da abin ya fi shafa, ciki har da Arewacin Darfur da Kudancin Kordofan, iyalai na shafe kwanaki ba tare da cin komai ba, sannan suna komawa ga cin ganye da abincin dabbobi domin su rayu.
Gargaɗi kan matsananciyar yunwa
Hukumomin agaji sun yi gargaɗin cewa ba wai rikici kaɗai ke rura wutar wannan matsala ba, ana lalata gonaki da kasuwanni da gangan, lamarin da ke sanya fargabar cewa ana amfani da yunwa a matsayin makamin yaƙi.
Fiye da mutane miliyan 28 — wanda ya kai kusan kashi biyu cikin uku na al’ummar Sudan — suna cikin mawuyacin halin rashin abinci a yanzu, yayin da aka tabbatar da bullar matsananciyar yunwa a wasu sassan ƙasar.
Duk da kwararan shaidun da ake da su, gwamnatin Sudan ta musanta kasancewar matsananciyar yunwa a ƙasar, yayin da dakarun da ke yaƙar juna suke kauce wa ɗaukar alhakin halin da ake ciki a yankunan da ke ƙarƙashin ikon su.
Mata da yara ne abin ya fi shafa
Wannan matsala ta fi shafar mata da yara. Iyalai waɗanda mata ke jagoranta sun ninka sau uku wajen fuskantar barazanar rashin abinci, yayin da mata ke fuskantar haɗarin cin zarafi lokacin da suke ƙoƙarin neman abinci ko ruwa.
A lokaci guda kuma, ayyukan agaji na neman gazawa sakamakon rage kuɗaɗen tallafi, wanda hakan ke iyakance ayyukan jin ƙai, yayin da gidajen abinci na sa-kai ke fafutukar ciyar da dimbin mutanen da yawansu ke ƙaruwa.