Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai bar birnin Abuja zuwa Turai don fara hutun makonni uku a wani ɓangare na hutunsa na shekara-shekara.
Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan watsa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Lahadi ta ce shugaban na Nijeriya zai ziyarci Landan a tafiyarsa a Turai ɗin.
ZA KU SO WAƊANNAN
“Ana tsammanin Shugaba Tinubu ya dawo gida bayan hutun aikin domin shiga fafatukar yaƙin neman zabe na zaben watan Janairun shekarar 2027,” in ji sanarwar Onanuga.




















