| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Fiye da mutum 1,000 ne suka tsere wa hare-haren 'yanbindiga a jihar Benue ta Nijeriya
Maharan sun afka wa al'ummar Ankpechi da ke gundumar Oglewu ta karamar hukumar Ohimini a safiyar Alhamis, inda suka tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu su nemi mafaka a al'ummomin da ke makwabtaka, a cewar jami'an yankin.
Fiye da mutum 1,000 ne suka tsere wa hare-haren 'yanbindiga a jihar Benue ta Nijeriya
Benue, na daya daga cikin manyan jihohin da ake noma a Nijeriya, ta fuskanci rikice-rikice da ke da alaka da kungiyoyi masu dauke da makamai

Fiye da mutum 1,000 ne suka tsere daga gidajensu bayan da wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne suka kai hari ga al’ummar Ankpechi da ke jihar Benue a yankin arewa maso tsakiyar Nijeriya, kamar yadda mazauna yankin suka bayyana a ranar Alhamis, a daidai lokacin da wani sabon tashin hankali ya afka wa yankin da ke samar da abinci a Nijeriya.

Maharan sun afka wa al'ummar Ankpechi da ke gundumar Oglewu ta Ƙaramar Hukumar Ohimini a safiyar Alhamis, inda suka tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu su nemi mafaka a al'ummomin da ke makwabtaka, a cewar jami'an yankin.

Garin yana a hanyar Otukpo–Ogobia sannan tana kusa da Ondo-Ugboju a Karamar Hukumar Otukpo, inda a kwana nan 'yan bindiga suka kona wasu gidaje.

Kazalika, Shugaban Karamar Hukumar Ohimini, Gabriel Adole, ya tabbatar da harin.

Neman mafaka a al'ummomin da ke kusa

"Mahara sun mamaye al'ummar a safiyar Alhamis," kamar yadda Adole ya shaida wa manema labarai a Makurdi, babban birnin jihar ta Benue.

Ya ce an kori mazauna yankin daga gidajensu sakamakon harin kuma suna neman mafaka a al'ummomin da ke kusa, yayin da aka tura jami'an tsaro zuwa yankin don dakile sake aukuwar hare-haren.

Harin na baya-bayan nan ya zo ne kwanaki kaɗan bayan wasu munanan hare-hare da aka kai yankin karamar hukumar Otukpo da ke makwabtaka da jihar, lamarin da ke nuna karuwar rashin tsaro a sassan jihar Benue, inda kungiyoyi masu dauke da makamai suke yawan kai hari kan kauyuka, sannan suna kashe mazauna, tare da lalata gidaje, da kuma tilasta wa dubban mutane tserewa.

Benue, na ɗaya daga cikin manyan jihohin da ake yin noma a Nijeriya, kuma ta fuskanci rikice-rikice da ke da alaƙa da ƙungiyoyi masu dauke da makamai da kuma takaddamar da ta dade tana faruwa kan gonaki da dabbobin da ake kiwo.

Hare-haren da ake yawan kai wa sun raba dubban mutane da muhallinsu, sannan sun janyo cikas ga ayyukan noma da kara dagula yanayin ayyukan jinƙai a faɗin jihar.