Jami'an tsaron Turkiyya sun ce Turkiyya ta ƙarfafa tsarin yadda take tura sojojinta zuwa Somaliya, inda ta faɗaɗa rundunonin sama da na ƙasa waɗanda aka ɗora musu nauyin tallafa wa ƙasar da ke yankin kusurwar Afirka wadda ke yaƙi da ta'addanci, yayin da hare‑haren ke ƙaruwa a ciki da kewaye da babban birnin Mogadishu.
Jami'an tsaron na Turkiyya a ranar Alhamis sun ce Rundunar Hadin Gwiwar Somaliya da Turkiyya da Sashen Rundunar Sojin Sama na Turkiyya suna ci gaba da inganta ƙarfin Somaliya na yaki da ta'addanci ta hanyar tallafin soja, horo da ayyukan ba da shawara.
Sun ce an ƙarfafa Rundunar Sojin Saman Turkiyya da ke Somaliya ta hanyar aika ƙarin soji da kayayyakin aiki, inda za su taimaka wurin ci gaba da daƙile ta’addanci.
Yakin Somaliya da al-Shabaab
Somaliya na fama da 'yan ta'addar al-Shabaab fiye da shekaru goma, kungiyar da ke da alaƙa da al-Qaeda.
Duk da ci gaba da ayyukan soji da dakarun Somaliya ke yi da dakarun Tarayyar Afirka da dakarun ƙasashe ƙawaye, kungiyar na ci gaba da kai hari ta hanyar tayar da bama-bamai da aikata kisan kai, musamman a Mogadishu da yankunan kusa da birnin.
A cikin 'yan watannin baya‑bayan nan, al-Shabaab ta ƙara yawan hare‑harenta kan hukumomin gwamnati, jami'an tsaro da wuraren taron jama'a, abin da ke nuna yadda kungiyar ke iya amfana da gibin tsaro ko da hukumomin Somaliya na ci gaba da farautar mayaƙan a ƙasar baki ɗaya.
Ci gaba da tallafin Turkiyya
Turkiyya ta zama ɗaya daga cikin abokai mafi kusa na Somaliya, inda take da babban sansanin horar da soji a Mogadishu tare da ba da babban tallafi ga Sojin Kasa na Somaliya.
Malaman Turkiyya sun horar da dubban sojojin Somaliya, kuma Ankara ta samar da kayan aiki, taimakon fasaha da jagorancin ayyuka.
Jami'an Turkiyya na cewa manufar ita ce taimaka wa Somaliya gina tsarin tsaro mai ɗorewa wanda zai iya tabbatar da zaman lafiya na dogon lokaci da rage dogaro ga ƙungiyoyin ƙetare.
Ƙarin tura mayakan da aka yi na baya‑bayan nan na nuna nufin Ankara na zurfafa wannan haɗin gwiwa a wani muhimmin lokaci, yayin da hukumomin Somaliya ke ƙoƙarin tabbatar da nasarori kan al-Shabaab da hana kungiyar sake samun yankuna.


















