Aƙalla kimanin mutane 50 ne suka mutu bayan wani kwale-kwale ya kife a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Nijeriya a ranar Alhamis, kamar yadda wani mazaunin yankin ya shaida wa AFP, yayin da hukumomi suka ce ana ci gaba da ayyukan ceto.
Hatsarin ya faru ne a safiyar Alhamis lokacin da fasinjoji a cikin jirgin - wanda ake cewa an yi masa lodi fiye da ƙima - ke kan hanyar zuwa gona aikin shinkafa, in ji Sarkin Daji, wani shugaba na gargajiya a yankin.
Irin waɗannan hadurra sun zama ruwan dare a koguna da hanyoyin ruwa da ke cike da jama'a a Nijeriya, galibi suna faruwa ne sakamakon cika kwale-kwale, da rashin kulawa ko kuma rashin bin ka'idojin kariya.
"Yanayin ya yi muni," in ji Ibrahim Musa, tsohon kansilan ƙauyen Gorau, a gundumar Goronyo, inda hatsarin ya faru.
"Mun riga mun binne gawawwaki 46, kuma an fitor da wasu biyar daga kogin," in ji shi.
"Masu iyo na yankin sun samo gawawwaki, kuma har yanzu ana ci gaba da laluben waɗanda suka nutse," in ji wani mazaunin garin Nasiru Gorau.
Dahir Kure, mai magana da yawun Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa a jihar, ya shaida wa AFP, cewa ana ci gaba da ayyukan ceto.
"Yanzu muna wurin da hatsarin jirgin ruwan ya faru kuma mun fara aikin ceto," in ji Kure.
Kure ya ce ba zai iya bayar da rahoton asarar rayuka nan take ba, yana mai cewa hukumomi har yanzu suna "tattara bayanai masu mahimmanci game da lamarin".
A watan Janairu, aƙalla mutane 26 ne suka nutse lokacin da kwale-kwalen da ke dauke da manoma da masunta daga Jigawa zuwa jihar Yobe ya kife.
















